Sarakunan Gargajiya daga Ketare Sun Shiga Fadar Sanusi II, Sun Yi Masa Mubaya'a

Sarakunan Gargajiya daga Ketare Sun Shiga Fadar Sanusi II, Sun Yi Masa Mubaya'a

  • Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya samu mubaya'a daga manyan sarakunan gargajiya daga Jamhuriyar Nijar da jihar Yobe
  • Sarakunan daga Yobe sun hada da Sarkin Machina Alhaji Bashir Albishir Bukar da Mai Jajere Alhaji Hamza Buba Mashigo
  • Daga Nijar kuwa akwai Abdu Kachalla Gasa Maine Dipa, Bubakar Yahaiya Lushe Bande, Abubakar Marafa Kyasa Tsibiri da Hassan Musa Angu Baraguine

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II na ci gaba da samun goyon baya daga manya da kuma sarakunan gargajiya.

Wasu sarakunan gargajiya daga ketare ma sun shiga har fadar basaraken a kano inda suka nuna goyon bayansu gare shi.

Sanusi II ya samu goyon baya daga sarakuna
Sarakuna daga Yobe da Nijar sun yi wa Sanusi II mubaya'a. Hoto: Sanusi II Dynasty.
Source: Twitter

Manyan sarakuna sun yiwa Sanusi II mubaya'a

Shafin Sanusi II Dynasty ne ya tabbatar da haka a yammacin yau Lahadi 10 ga watan Agustan 2025 a manhajar Facebook.

Kara karanta wannan

An yi rashi a Najeriya, babban Sarki ya yi bankwana da duniya yana da shekaru 82

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta ce manyan sarakunan gargajiya daga Jamhuriyar Nijar da dama sun yi mubaya'a ga Sarki Sanusi II a Kano.

Har ila daga cikin wadanda suka yi mubaya'ar akwai sarakunan gargajia daga jihar Yobe a Arewa maso Gabashin Najeriya.

Sarakunan daga sun hada na Machina, Alhaji Bashir Albishir Bukar, da Mai Martaba Mai Jajere, Alhaji Hamza Buba Mashigo.

Sanarwar ta ce:

"Masu martaba sarakunan gargajiya a Jamhuriyar Nijar da na Jihar Yobe sun kai ziyarar mubaya’a ga Mai Martaba Sarkin Kano.
"Sarakunan sun ziyarci Khalifa Dr. Muhammad Sanusi II, a fadar sa da yammacin yau, Lahadi 10 ga watan Agustan 2025.
"Wadanda suka halarta daga Jihar Yobe sun haɗa da Mai Martaba Sarkin Machina, Alhaji Bashir Albishir Bukar, da Mai Martaba Mai Jajere, Alhaji Hamza Buba Mashigo."
Sarakunan gargajiya sun yi mubaya'a ga Sanusi II
Sark Sanusi II ya samu goyon bayan sarakunan gargajiya. Hoto: Sabusi II Dynasty.
Source: Facebook

Sarakunan da suka ziyarci Sanusi II

Har ila yau, an jero sarakunan da suka kai ziyara fadar Sarki Sanusi II daga Jamhuriyar Nijar domin nuna masa mubaya'a.

Kara karanta wannan

Fitaccen mawaki a Arewacin Najeriya, Ali Jita ya zama mai unguwa a Kano

An lissafo sarakunan gargajiyan kamar haka, Mai Martaba Abdu Kachalla Gasa Maine Dipa, Mai Martaba Bubakar Yahaiya Lushe Bande na Zinder.

Sannan akwai Mai Martaba Abubakar Marafa Kyasa Tsibiri na Dosso, Mai Martaba Hassan Musa Angu Baraguine na Zinder.

Majiyoyi sun kuma tabbatar da cewa a cikin masu ziyarar akwai mai ba shugaban Nijar shawara, Bubakar Hassan.

"Daga Jamhuriyar Nijar kuma sun haɗa da Mai Martaba Abdu Kachalla Gasa Maine Dipa, Mai Martaba Bubakar Yahaiya Lushe Bande na Zinder.
"Sai kuma Mai Martaba Abubakar Marafa Kyasa Tsibiri na Dosso, Mai Martaba Hassan Musa Angu Baraguine na Zinder, tare da Bubakar Hassan, mai ba wa shugaban ƙasar Nijar shawara."

- Cewar Sanarwar

Sarkin Kofa ya yi mubaya'a ga Sanusi II

Kun ji cewa Balarabe Sarkin Kofa ya tuba a gaban Sarkin Kano na 16, Khalifa Muhammad Sanusi II saboda rashin biyayya da ya nuna a baya.

Rahotanni sun nuna cewa a gaban manyan 'yan fada ya furta kalmomin tuba tare da yin mubaya’a ga Mai Martaba Sarkin.

Ya janye goyon bayansa ga fadar Nasarawa, ya kuma bukaci afuwa bisa goyon bayan da ya baiwa Aminu Ado Bayero a baya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.