Rikici Ya Kaure tsakanin Dogo Gide da Hatsabibin Ɗan Bindiga, an Kashe Wasu

Rikici Ya Kaure tsakanin Dogo Gide da Hatsabibin Ɗan Bindiga, an Kashe Wasu

  • Rikicin da ya barke tsakanin Dogo Gide da Kachalla Alti a Tsafe, Zamfara, ya yi sanadiyyar mutuwar mutane biyu da sace wasu shida
  • Rahotanni sun ce maharan sun tilasta wa mazauna kauyuka aiki a gonar Dogo Gide, inda Kachalla Alti ya kai farmaki ya yi garkuwa
  • Daga baya jami’an tsaro sun ceto wani da ya jikkata tare da samun gawarwaki biyu, yayin da aka saki fursunoni da yamma.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Gusau, Zamfara - Harin ’yan bindiga da aka kai kwanan nan a karamar hukumar Tsafe ta Zamfara ta rikita jama'a a jihar.

Wannan harin ya sake tabbatar da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma wanda ke ci gaba da tayar da hankulan al'umma.

An kaure da fasa tsakanin yan bindiga
Rikici tsakanin Dogo Gide da Alti sun kaure da fada. Hoto: Legit.
Asali: Original

An rasa rayuka bayan rikicin yan bindiga

Kara karanta wannan

An yi rashi a Najeriya, babban Sarki ya yi bankwana da duniya yana da shekaru 82

Majiyar tsaro ta shaida wa Zagazola Makama cewa lamarin ya fara ne da misalin ƙarfe 8:30 na safiyar Asabar 9 ga watan Agustan 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majiyoyi sun bayyana cewa harin da ya faru ranar 9 ga watan Agusta, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane biyu da sace wasu shida.

An ce hakan ya samo asali ne daga rikici tsakanin manyan ’yan bindiga Dogo Gide da Kachalla Alti.

Hakan ya faru ne lokacin da aka tilasta mazauna Keta, Kwaren Gabuwa da Bawa Ganga yin aiki a gonar Dogo Gide.

Yadda rigimar ta fara a Zamfara

Yayin da mutanen ke aiki a gonar da ke wajen Keta, wani jagoran ’yan bindiga, Kachalla Alti, ya kai hari mai ramuwar gayya inda ya sace mutane shida nan take.

Da yamma, da misalin ƙarfe 5:20, jami’an tsaro suka gano gawarwaki biyu tare da ceto wani mutum da ya samu raunuka sakamakon harbin bindiga.

Kara karanta wannan

Davido: Mawakin Najeriya ya yi auren kece raini, ya kashe sama da Naira biliyan 5

A cikin abin mamaki, an saki mutanen da aka sace da misalin ƙarfe 8:30 na dare, mai yiyuwa ne saboda tattaunawa ko yarjejeniya tsakanin kungiyoyin.

An kai gawarwakin da wanda ya jikkata zuwa Asibitin Gwamnati na Tsafe domin yin gwaji da kuma samun kulawar lafiya daga likitoci.

An rasa rayuka yayin fada da yan bindiga
An yi kazamar fada tsakanin Dogo Gide da Kachallah Alti. Hoto: Legit.
Asali: Twitter

Yan sa kai sun fara sintiri a Zamfara

A halin yanzu jami’an tsaro tare da ’yan sa-kai sun kara yawan sintiri a yankin domin dakile sake faruwar irin wannan hari.

Dogo Gide na daga cikin manyan masu ta’addanci da ke da ikon manyan hanyoyin aikata laifi a Zamfara, Katsina, Neja da wasu sassan Kaduna.

An alakanta shi da garkuwa da mutane, kisan gillar mutane da dama, da kuma kai hare-hare kan jami’an tsaro da wuraren aiki a jihohin Arewa maso Yamma.

Yan bindiga sun hallaka junansu a Zamfara

Kun ji cewa tawagar 'yan bindiga biyu ma su hamayya da juna sun kaure da faɗa tsakaninsu kan yunkurin kwace ikon wani yankin Zamfara.

Kara karanta wannan

Najeriya ta yi babban rashi, tsohon ministan Buhari, Audu Ogbeh ya rasu

Lamarin ya faru ne a wani jejin karamar hukumar Maru, jihar Zamfara inda ‘yan ta’addan suka yi kaurin suna wajen farmakar jama'a.

Majiyoyin leken asiri sun shaida cewa akalla ‘yan ta’adda 16 suka mutu a arangamar, ciki har da wasu manyan jagorori guda biyu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.