Jami'an Tsaro Sun Ragargaji 'Yan Bindiga a Bauchi, an Kashe Miyagu
- Jami'an tsaro sun samu nasarar mugun iri bayan sun yi artabu da 'yan bindiga a jihar Bauchi da ke yankin Arewa maso Gabashin Najeriya
- A yayin fafatawar da aka yi tsakanin bangarorin biyu, an samu nasarar tura 'yan bindiga guda biyu zuwa lahira
- Hakazalika, jami'an tsaron sun fatattaki ragowar 'yan bindigan zuwa cikin daji tare da kwato wasu daga cikin makaman da suke amfani da su
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Bauchi - An samu nasarar kashe 'yan bindiga yayin wani gagarumin aikin haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da aka gudanar a jihar Bauchi.
Jami'an tsaron sun kashe 'yan bindiga guda biyu tare da kwato bindigar AK-47 daga hannunsu a karamar hukumar Alkaleri.

Source: Twitter
Masani kan harkokin tsaro a yankin Tafkin Chadi da Arewacin Najeriya, Zagazola Makama, ya bayyana hakan a shafinsa na X.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Jami'an tsaro sun fafata da 'yan bindiga
Lamarin dai ya auku ne a ranar Juma'a, 8 ga Agusta, 2025 bayan an gwabza fada tsakanin jami'an tsaro da 'yan bindiga.
Rahotanni sun nuna cewa da misalin ƙarfe 4:00 na yamma, jami'an tsaro da suka hada da 'yan sa-kai sun hango wasu ’yan bindiga guda shida a tsakanin ƙauyen Dogon Ruwa da dajin Yakaki.
Jami'an tsaron sun hango 'yan bindigan ne dai dauke da makamai yayin wani aikin sintiri na yau da kullum.
Bayan ganin waɗanda ake zargi, tawagar jami’an tsaro tare da ’yan sa-kai sun bi sawunsu a hankali, inda suka shirya musu kwanton ɓauna.
Wannan mataki ya haifar da musayar wuta mai tsanani amma ta ɗan gajeren lokaci.
A yayin wannan arangama, an kashe ’yan bindiga biyu a wurin, yayin da sauran huɗun suka tsere cikin dajin da ke kusa.
Haka kuma, jami’an tsaro sun kwato bindigar AK-47 ɗaya wadda ba ta da harsasai daga hannun waɗanda aka kashe.
Bayanan da suka fito daga jami’an tsaro sun nuna cewa wannan aikin ya kasance sakamakon ƙarin haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro da al’ummar yankin.
Lamarin ya kara fito da irin muhimmiyar rawar kungiyoyin sa-kai ke takawa wajen taimaka wa gwamnati kan yaki da ta’addanci da satar mutane a yankunan karkara.

Source: Original
Karanta wasu labaran kan 'yan bindiga
- Tashin hankali: 'Yan bindiga sama da 200 sun farmaki ofishin 'yan sanda a Kwara
- 'Yan bindiga sun titsiye Sarki a dajin Zamfara, ya amsa tambayoyi masu zafi
- Ana batun sulhu da Turji, Gwamna Bago ya fadi matsayarsa kan tattaunawa da 'yan bindiga
'Yan bindiga sun sace matafiya
A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu 'yan bindiga sun tare matafiya suna tsaka da tafiya kan wata hanya a jihar Kogi.
'Yan bindigan sun yi awon gaba da wasu daga cikin fasinjojin motar bayan sun bude musu wuta.
Sai dai, direban motar da wasu daga cikin 'yan bindigan sun samu nasarar tsira daga kamun 'yan bindigan bayan sun gudu zuwa cikin daji.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

