Namadi: Kakkausar Gargadin Abba Kabir ga Mukarrabansa, Ya Ja Layi a Gwamnatinsa

Namadi: Kakkausar Gargadin Abba Kabir ga Mukarrabansa, Ya Ja Layi a Gwamnatinsa

  • Gwamna Abba Kabir Yusuf ya gargadi jami’an gwamnati su guji duk wani abu da zai bata sunan gwamnatinsa
  • Ya bayyana hakan ne bayan murabus da kwamishinan sufuri Ibrahim Namadi Dala saboda alaka da wanda ake zargi da safarar kwayoyi
  • Gwamnan ya ce gwamnati ba za ta lamunci taimakon masu laifi ba kuma duk mai hannu zai fuskanci hukunci

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Bayan murabus din kwamishina a Kano, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tura gargadi ga mukarrabansa.

Gwamnan ya ce dole ne kowa ya zama mai gaskiya da rikon amana domin guje wa abubuwan da za su bata sunan gwamnati ko jefa matasa cikin hadari.

Abba Kabir ya tura gargadi mai zafi ga mukarrabansa
Gwaman Abba Kabir ya gargadi jami'an gwamnatinsa bayan murabus din Ibrahim Namadi. Hoto: Abba Kabir Yusuf.
Asali: Facebook

Hakan na cikin wata sanarwa da sakataren yada labaransa, Sanusi Bature D-Tofa ya bayyana a shafinsa na Facebook.

Kara karanta wannan

Ibrahim Namadi da kwamishinonin Kano 2 da suka ajiye aiki a gwamnatin Abba Yusuf

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Namadi ya yi murabus daga gwamnatin Abba

Hakan ya biyo bayan murabus din kwamishinan sufuri na jihar Kano, Alhaji Ibrahim Namadi Dala.

Ana zargin Namadi da alaka da masu safarar kwaya bayan ya yi belin shahararren mai sayar da kwaya, Sulaiman Danwawu.

Daga bisani, Abba Kabir ya kafa kwamitin bincike domin sanin dalilin belin dan kwayar bayan ce-ce-ku-ce daga al'umma.

Murabus din kwamishina ya jawo jan kunne a gwamnatin Abba Kabir
Abba Kabir ya gargadi mukarrabansa bayan murabus din Ibrahim Namadi. Hoto: Abba Kabir Yusuf.
Asali: Facebook

Abba ya fadi darasin dauka daga Namadi

Abba Kabir ya bayyana haka ne a yayin taron majalisar zartarwa karo na 30 da aka gudanar a gidan gwamnati Kano ranar Laraba, 6 ga watan Agusta, 2025.

Ya ce murabus da kwamishinan ya zama darasi ga sauran masu rike da madafun iko a jihar domin kauce wa aikata sabawa doka.

Sanarwar ta ce:

“Ba za mu yarda wani jami’i ya aikata laifi ko wani abu da zai kawo cikas kan abin da muka sanya a gaba ba, ko waye ne zai fuskanci hukunci."

Kara karanta wannan

Belin dilan ƙwaya: Kwamishinan Abba a jihar Kano ya yi murabus

Alkawuran Abba Kabir Yusuf ga 'yan Kano

Gwamna Abba ya ce duk wanda bai iya rike amana ba ya fi dacewa ya ajiye aiki tun kafin ya jawo wa gwamnati abin kunya.

Ya jaddada cewa yakin da gwamnati ke yi da safarar kwayoyi da miyagun dabi’u yana daga cikin ginshikan mulkinsa.

Ya ce duk wanda aka samu yana taimaka wa masu laifi kai tsaye ko a boye zai gamu da fushin doka ba tare da sassauci ba.

A ƙarshe, Gwamna Abba ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da kare gaskiya, adalci da bauta wa al’ummar Kano.

Bayana sun fito kan Ibrahim Namadi a Kano

Kun ji cewa rahoton Hukumar DSS ya sake bankado wasu bayanai game da Kwamishinan sufuri na Kano, Ibrahim Namadi game da belin dan kwaya.

An bayyana cewa Kwamishinan ya karɓi $30,000 daga Sulaiman Danwawu da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi wanda ya jawo magana a jihar da Najeriya baki daya.

Gwamna Abba Yusuf ya fusata da wannan batu tare da kafa kwamiti, duk da cewa Namadi yana da dangantaka da Rabiu Kwankwaso wanda ake zargin ya hana daukar mataki mai tsauri.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.