Sanusi II Ya Rufe Bakin Mutane, Ya Je Gidan Buhari domin Yin Ta'aziyya ga Iyalansa

Sanusi II Ya Rufe Bakin Mutane, Ya Je Gidan Buhari domin Yin Ta'aziyya ga Iyalansa

  • An tabbatar da rasuwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a London, inda aka yi jana'izarsa a Daura ranar Talata 15 ga Yuli, 2025
  • Ce-ce-ku-ce ya biyo bayan rashin ganin Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, a jana’izar, sai dai daga baya ya kai ziyarar ta’aziyya a Kaduna
  • Mai Martaba Sanusi II ya bayyana cewa yana halartar taro ne a London lokacin da aka yi jana’izar marigayin, a yau ne ya je ya yi gaisuwa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kaduna - An tabbatar da rasuwar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari a ranar Lahadi 13 ga watan Yulin 2025.

Manyan yan siyasa da sarakunan gargajiya gargajiya sun samu halartar jana'izar marigayin a garin Daura da ke jihar Katsina.

Sanusi II ya ziyarci gidan Buhari
Sanusi II kai ziyarar ta'aziyya gidan Buhari a Kaduna. Hoto: Sanusi II Dynasty.
Source: Facebook

Shafin Sanusi II Dyansty ya wallafa a Facebook cewa Sarkin Kano, Sanusi II ya ziyarci gidan marigayi Buhari a Kaduna.

Kara karanta wannan

'Yan daba sun yi wa masoyin Sanusi II ta'addanci a Kano, Sarki ya tafi asibiti

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jana'izar Buhari: An yi ta magana kan Sanusi II

Sarkin ya kai wannan ziyara ne bayan ce-ce-ku-ce da aka ta yi a bayan lokacin rasuwar marigayin a birnin London

Babban abin da ya fara jawo magana shi ne rashin ganin Sarki Sanusi II a wajen jana'izar Buhari da aka yi a ranar 15 ga watan Yulin 2025.

Wasu na cewa masoyan Mai martaba Aminu Ado Bayero ne ke maganganu saboda Sanusi II bai samu halarta ba.

Sai dai shi kuma Aminu Ado na gaba cikin waɗanda suka halarci jana'izar a ranar Talata 15 ga watan Yulin 2025.

An fadi dalilin rashin ganin Sanusi II a Daura

Daga bisani, makusancin Sanusi II da ake kira Muhammadu Dalhatu ya fitar da sanarwa kan dalilin rashin ganin basaraken yayin jana'izar.

Ya ce Sanusi II yana halartar wani taro ne a birnin London wanda shi ne dalilin rashin samun damar zuwa Daura.

Kara karanta wannan

Sarautar Kano: Sarkin Kofa ya dawo bangaren Sanusi II, ya yi watsi da Aminu Ado

Bayan maganganu, Sanusi II ya ziyarci gidan Buhari
Sanusi II ya je har Kaduna ta'aziyya ga iyalan Buhari. Hoto: Sanusi II Dynasty.
Source: Twitter

Sanusi II ya ziyarci gidan Buhari a Kaduna

Sai dai a yanzu Sarkin ya ba marada kunya saboda tashi ya yi takanas ta Kano har gidan marigayin

Sarkin ya kai ziyarar ta'azziyar a yau Talata 5 ga watan Agustan 2025 domin jajantawa iyalan marigayin.

Yayin ziyarar, Sarkin ya yi musu jaje tare da addu'ar Ubangiji ya yi wa tsohon shugaban rahama da saka masa da gidan aljanna.

Sanarwar da aka fitar ta ce:

"Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammad Sanusi II, PhD, CON, ya kai ziyara gidan marigayi tsohon shugaban ƙasa, Janar Muhammadu Buhari, da ke Kaduna, domin yi wa iyalansa ta’aziyya.
"Sarki Sanusi II ya zai ziyarar a yau Talata, 5 ga watan Agustan shekarar 2025."

Sheikh Bello Yabo ya tabo batun yafewa Buhari

Mun ba ku labarin cewa Sheikh Bello Aliyu Yabo ya shawarci masu mulki su tuba kafin mutuwa, yana sukar wadanda ke neman a yafe wa Muhammadu Buhari.

Kara karanta wannan

Bayan barin kujerar APC, Hadimin Ganduje ya zargi Gwamnatin Tinubu da son kai

Sheikh Yabo ya ce rashin mayar da dukiyar da aka wawure da kuma karancin nadama yana nuna cewa an yi zalunci da cin hanci ne da gangan.

Malamin ya koka da yadda 'yan Najeriya ke yafewa duk da halin kunci, yana cewa Allah ma yana da sharudda kafin yafewa mai zalunci.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.