Dakarun Sojoji Sun Ritsa 'Yan Boko Haram a Daji, an Hallaka Miyagu

Dakarun Sojoji Sun Ritsa 'Yan Boko Haram a Daji, an Hallaka Miyagu

  • Dakarun sojojin Najeriya masu aikin samar da tsaro a yankin Arewa maso Gabas sun samu nasara kan 'yan ta'addan Boko Haram a jihar Borno
  • Sojojin na rundunar Operation Hadin Kai sun yi nasarar hallaka 'yan ta'adda bayan sun yi musayar wuta yayin wani aikin sintiri
  • Wannan na zuwa ne yayin da jami'an tsaro ke kara kaimi wajen kawo karshen ayyukan ta'addanci a jihar Borno

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Borno - Dakarun sojoji na sashe na biyu na rundunar Operation Hadin Kai (OPHK), tare da haɗin gwiwar ’yan sa-kai na CJTF sun hallaka ‘yan ta’adda uku na Boko Haram/ISWAP a jihar Borno.

Dakarun sojojin sun hallaka 'yan ta'addan ne a yayin wani dogon sintiri na fatattakar miyagu a jihar Borno.

Sojoji sun kashe 'yan Boko Haram
Dakarun sojoji sun hallaka 'yan Boko Haram Hoto: @HQNigerianArmy
Source: Twitter

Masani kan harkokin tsaro a yankin Tafkin Chadi da Arewacin Najeriya, Zagazola Makama, ya bayyana hakan a shafinsa na X.

Kara karanta wannan

Gwara Haka: Jagororin 'yan bindiga sun gwavza fada a Zamfara, an samu asarar rayuka

Sojoji sun hallaka 'yan ta'addan Boko Haram

Majiyoyi sun bayyana cewa aikin sintirin wanda ya kutsa cikin dajin Bulabulin har zuwa yankin Magumeri, ya janyo musayar wuta mai tsanani a kusa da yankin Borno Yesu.

Majiyar ta bayyana cewa bangaren sojojin sama na rundunar Operation Hadin Kai ya bayar da goyon baya ta sama da kuma tsare-tsare na sa ido yayin fafatawar, wanda hakan ya ba dakarun damar mamaye matsugunin ‘yan ta’addan.

"Bayan arangamar, an kashe ‘yan ta’adda uku. Dakarun sun kwato bindigogi kirar AK-47 guda uku, makamai guda huɗu da aka cika da harsasai, harsasai 120 masu kaurin 7.62mm, gurneti, jakunkunan yaki da sababbin babura guda biyu."
"Tawagar kwararrun sojoji na musamman na ci gaba da mamaye yankin, suna ƙara matsin lamba domin kara fatattakar ‘yan ta’adda, da yanke hanyoyin samun kayayyaki, da hana su ‘yancin yin yawo."

- Wata majiya

Sojoji na kokarin kawar da 'yan ta'adda

Majiyar ta ƙara da cewa, kwarin gwiwar dakarun da kuma kwarewarsu a fagen fama suna nan daram yayin da aikin kawar da ’yan ta’addan ke ci gaba.

Kara karanta wannan

Ba sauki: Dakarun sojoji sun hallaka manyan kwamandojin 'yan ta'adda

Sojojin Najeriya sun ƙara zafafa hare-hare a yankin Arewa maso Gabas domin dawo da zaman lafiya da kuma bada damar komawar al’ummomin da rikicin ya raba da muhallansu cikin aminci.

Sojoji sun kashe 'yan Boko Haram a Borno
Sojoji sun hallaka 'yan ta'addan Boko Haram Hoto: Legit.ng
Source: Original

Karanta karin wasu labaran kan sojoji

'Yan bindiga sun hallaka sojoji

A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu miyagun 'yan bindiga sun hallaka jami'an sojoji da 'yan sa-kai a jihar Plateau.

'Yan bindigan sun hallaka jami'an tsaron ne bayan sun yi musu kwanton bauna lokacin da suke kan hanyar kai agajin gaggawa.

Mummunan kwanton baunan ya yi sanadiyyar rasa ran sojoji biyu da 'yan sa-kai biyu bayan an kwashi lokaci ana arangama.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng