Dara Ta ci Gida: Kotu Ta Umarci Ƴan Sanda Su Biya Masu Zanga Zanga Diyyar N10m

Dara Ta ci Gida: Kotu Ta Umarci Ƴan Sanda Su Biya Masu Zanga Zanga Diyyar N10m

  • Wata kotu a Lagos ta umarci babban Sufetan yan sanda ya biya N10m ga masu zanga-zangar EndSARS bisa take hakkinsu na 'yan kasa
  • Alkalin kotu ya ce ’yan sanda sun ci zarafin masu zanga-zanga duk da ’yancinsu na taro da walwala bisa kundin tsarin mulki
  • Masu kara sun hada da kungiyoyi da dama kamar ERC, TIB da CDHR da wasu mutane 23 da aka ce an ci zarafinsu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ikeja, Lagos - Wata kotu a ranar Alhamis 24 ga watan Yulin 2025 ta yi zama kan shari'ar da ake karar rundunar yan sanda.

Mai Shari'a, Musa Kakaki na Babbar Kotun Tarayya da ke Lagos, ya ci tarar rundunar yan sanda saboda cin zarafin masu zanga-zanga.

An ci tarar yan sanda N10m kan cin zarafin masu zanga-zanga
Kotu ta umarci ƴan sanda biyan masu zanga-zanga N10m. Hoto: Nigeria Police Force.
Source: Twitter

Matakin da kotu da dauka kan yan sanda

Kara karanta wannan

Kano: Kotun tarayya ta tunkuɗa ƙeyar ɗan TikTok, G Fresh zuwa gidan kaso

Leadership ta ce alkalin ya umurci Sufeto Janar na ’Yan sanda da ya biya N10m a matsayin diyyar cin zarafinsu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakan ya biyo bayan zanga-zangar wasu masu fafutukar rajin sauyi da suka halarci bikin cika shekara hudu na zanga-zangar EndSARS.

Yayin da yake yanke hukunci a karar da masu fafutukar suka shigar, alkalin ya ce masu karar suna da ’yancin taro da walwala kamar yadda sashe na 40 na kundin tsarin mulkin 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima) ya tanada.

Gargadin kotu ga 'yan sanda kan bin doka

Kotun ta kuma bayyana cewa, ko da yake ’yan sanda na da ikon aiwatar da doka, dole su yi hakan bisa ka’idar dimokuradiyya da dokar kasa.

Kotun ta kara da cewa an ci zarafin masu karar, wadanda suka halarci zanga-zangar a ranar 20 ga Oktoba, 2024, ba bisa ka’ida ba kuma an tauye musu ’yancin su.

Ana zargin yan sanda da cin zarafin masu zanga-zanga
Kotu ta ci tarar yan sanda N10m kan cin zarafin masu zanga zanga. Hoto: Nigeria Police Force.
Source: Facebook

Zanga-zanga: Wadanda ke karar rundunar yan sanda

Masu karar sun hada da Uadiale Kingsley, Ilesanmi Kehinde, Osopale Adeseye, Olamilekan Sanusi, Hassan Taiwo Soweto, cewar The Guardian.

Kara karanta wannan

'Kwankwaso na tsaka mai wuya a siyasa tsakanin shiga APC, PDP ko ADC,'

Sai kuma Akin Okunowon, Ugochukwu Prince, Osugba Blessing, Kayode Agbaje, Michael Adedeji, Jennifer Rita Obiora, Orunsola Oluremi, Seyi Akinde da Aisha Omolara.

Sauran sun hada da Isaac Obasi, Funmilayo Jolade Ajayi, Thomas Abiodun Olamide, Ogbu Obinna Ferdinald, Aghedo Kehinde Stephen, Duronike Olawale, Gideon Adeyemi, da Afeez Suleiman.

Har ila yau, daga cikin kungiyoyi masu karar akwai 'Campaign for the Defence of Human Rights (CDHR)', 'Education Rights Campaign (ERC)' da 'Take It Back Movement (TIB)'.

An gudanar da zanga-zangar tsofaffin 'yan sanda

A wani labarin, tsofaffin ‘yan sanda na kasa sun isa Abuja domin gudanar da babbar zanga-zanga saboda tsarin kudin fansho wanda ake zargin babu tsari a cikinsa.

'Dan takarar shugaban kasa na AAC, Omoyele Sowore, da wasu masu fafutuka sun gudanar da zanga-zanga a birnin tarayya wanda aka shirya musamman saboda tsofaffin yan sanda.

Rundunar ‘yan sanda ta zargi wasu da amfani da batun jin dadin jami’an da suka yi ritaya don cimma wata manufa ta su ta karan kansu da ta ganin ya saba doka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.