Gwamnoni 3 da Sarkin Kano Za Su Halarci Muhimmin Taron Musulunci na Kwana 2

Gwamnoni 3 da Sarkin Kano Za Su Halarci Muhimmin Taron Musulunci na Kwana 2

  • Makarantar Al-Faidiyyah mai koyar da ilimin addinin musulunci da Larabci ta shirya bikin cika shekaru 60 da kafuwa a Legas
  • Bikin wanda zai shafe kwanaki biyu, ana sa ran zai samu halartar manyan baki ciki har da gwamnonin Kano, Katsina da Neja
  • Mai martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II na cikin sarakunan da ake sa ran ganinsu a wannan taro

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Legas - Gwamnonin jihohin Kano, Neja da Katsina na daga cikin manyan baki da ake sa ran za su halarci bikin cika shekaru 60 da kafuwar Makarantar Al-Faidiyyah ta Karatun Larabci da Addinin Musulunci a Lagos.

Gwamnonin da suka haɗa da Alhaji Abba Kabir Yusuf (Kano), Mohammed Umar Bago (Neja) da Dikko Umar Radda (Katsina) za su halarci wannan taro na musulunci.

Kara karanta wannan

Tinubu ya yi bayani yayin da aka fara taron daidaita farashin fetur a Abuja

Makarantar koyar da musulunci da larabci a Legas ta cika shekara 60 da kafuwa.
Sarkin Kano da gwamnoni 3 za su halarci taron makarantar addinin Musulunci a Legas Hoto: Legit.ng
Source: Original

A cewar masu shirya taron, wannan bikin zai gudana na tsawon kwanaki biyu, daga 26 zuwa 27 ga watan Yuli 2025, kamar yadda Leadership ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sarkin Kano zai haɗu da gwamnoni 3 a Legas

Ana sa ran taron zai sami halartar manyan sarakuna kamar Oba Rilwan Akiolu na Lagos, Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II.

Haka zalika za a ga Farfesa Ibrahim Ahmad Makari, Babban Limamin Masallacin Ƙasa da ke Abuja.

An kafa makarantar shekaru 60 da suka wuce ta hannun marigayi Sheikh Imam Mukhtar Danlami, ta shahara a matsayin jagora kuma fitacciyar cibiyar ilimin addini musamman a tsakanin Hausawa da ke kudancin Najeriya.

A bana, makarantar za ta yaye dalibai kusan 120 waɗanda suka kware wajen karatun Al-ƙur’ani kuma suka kammala matakin ilimin firamare.

Dalilin kafa makarantar Al-Faidiyyah

Musa Ibn-Saidu, mataimakin shugaban kungiyar iyaye da malamai ta makarantar (PTA), ya jaddada muhimmancin ilimin addinin musulunci da na Larabci a cikin al’umma.

Kara karanta wannan

Batan maciji ya birkita ƴan Kano, Sanusi II ya roƙi kwamishinan ƴan sanda alfarma

“Nan unguwar Agege ce, yankin da ke da yawan jama’a a Lagos. Yara da dama ba sa zuwa makarantar zamani.
"Abin da kawai za mu iya yi don taimaka musu shi ne mu kawo su nan, mu koya musu ilimi kuma mu hana su yawon banza a titi, ta haka muna rage aikata munanan dabi’u,” in ji shi.
Gwamna Abba, Sarki Sanusi da Malam Dikko Radda.
Taron makarantar koyar da ilimin addinin islama zai tara manyan mutane a Legas Hoto: Abba Kabir Yusuf, Masarautar Kano, Dr. Dikko Umaru Radda
Source: Facebook

Wace gudummuwa makarantar take bayar wa?

Ya bayyana cewa idan ba a tura matasa makaranta ba, suna iya fadawa cikin mummunar mu’amala da abokai, wanda hakan na iya jawo su shiga amfani da miyagun kwayoyi, sata da sauran laifuffuka.

"Rashin aikin yi ko rashin sanya su a makaranta yana iya jawo wa jiha matsala. Yanzu da wayoyin zamani ke yawo, kowanne yaro na so ya mallaki wayar salula, amma ba sa yin halastattun abubuwa da su.
"Saboda haka, ta hanyar wannan ilimin da muke bayarwa a araha, za mu iya hana su zaman banza a titi, sannan bayan makaranta mu taimaka musu da ayyuka da za su rika yi, don rage zaman banza.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya isa fadar shugaban kasa taron da ake sa ran Tinubu zai halarta

- Inji Musa Ibn-Saidu.

Sanusi II ya buɗe sabon masallacin Juma'a a Kano

A wani labarin, kun ji cewa Sarkin Kano na 16, Khalifa Muhammadu Sanusi II ya jagoranci bude sabon masallacin Jumu’a a Zawaciki da ke jihar Kano.

Mai Martaba Sarkin ya yi limancin Juma'a ta farko a sabon masallacin, inda ya yi huɗuba a ranar 18 ga watan Yuli, 2025.

Masarautar Kano, a wata sanarwa da ta fitar bayan buɗe masallacin, ta bayyana cewa an sanya wa sabon wurin iɓadar suna, 'masallacin Al-ansar Wal Muhajirun'.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262