Dangin Buhari Sun Lissafa Mutum 34 Sun Musu Godiya bayan Gama Zaman Makoki

Dangin Buhari Sun Lissafa Mutum 34 Sun Musu Godiya bayan Gama Zaman Makoki

  • Malam Mamman Daura ya gode wa Shugaba Bola Tinubu da matarsa bisa taimako kan rashin lafiya da rasuwar Muhammadu Buhari
  • Dangin Buhari sun nuna godiya ga kasashen duniya, sarakunan gargajiya da shugabannin addinai da suka jajanta musu
  • Iyalan sun ce irin addu’o’i da goyon bayan da suka samu sun kara musu kwarin gwiwa wajen jure babban rashin da suka yi

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Katsina - Mafi shekaru a dangin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, Malam Mamman Daura, ya yi godiya ga jama'a bayan gama zaman makoki.

Ya yi godiya ga ‘yan Najeriya da sauran mutane daga kasashe daban-daban da suka jajanta musu bayan rasuwar Buhari.

Dangin Buhari sun yi wa jama'a godiya
Dangin Buhari sun yi wa jama'a godiya. Hoto: Bashir Ahmad
Source: Facebook

Legit ta tattaro bayanan da Mamman Daura ya yi ne a cikin wano sako da aka wallafa a shafin tsohon shugaban kasar na X.

Kara karanta wannan

Sheikh Pantami ya yi kyautar ban mamaki da aka yi wa Buhari takwara a Bauchi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Godiya ga shugaban kasa da gwamnati

Malam Mamman Daura ya bayyana cewa dangin sun samu goyon baya daga shugaba Bola Ahmed Tinubu da uwargidansa, Sanata Remi Tinubu.

Haka zalika ya ce sun samu goyon bayan mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, wanda ya kai musu ziyara a Burtaniya da kuma Daura.

Malam Mamman Daura ya ce:

“Mun gode ƙwarai ga shugaban kasa bisa hukuncin da ya yanke na ayyana hutu da kuma yadda aka sake wa Jami’ar Maiduguri suna.
"Wannan gagarumin alheri ne da ya kara mana kwarin gwiwa.”

Haka zalika, ya nuna jin dadin yadda ministoci da sauran jami’an gwamnati suka nuna musu kulawa.

Godiya ga kasashen duniya da sarakuna

Dangin Buhari sun nuna godiya ga masu fada a ji daga sassan duniya kamar Sarki Charles III na Ingila.

Sun yi godiya ga Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya da mataimakiyarsa Amina Mohammed, shugaban kungiyar Tarayyar Afirka, da sauran shugabannin ECOWAS.

Kara karanta wannan

Bidiyo: Yadda aka fito da gawar Buhari daga jirgi da manyan mutanen da aka gani

Iyalan sun yi godiya ga sarakunan gargajiya da suka hada da Sultan na Sokoto, Shehun Borno, Sarkin Gwandu, da kuma manyan sarakunan Katsina da Daura.

Godiya ga Atiku, Dangote da sauransu

A cewar sanarwar, dangin sun gode wa tsofaffin mataimakan shugaban kasa Atiku Abubakar, Namadi Sambo, Farfesa Yemi Osinbajo.

Haka zalika sun godewa Babagana Kingibe, da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da sauran shugabannin majalisa.

Sun kuma nuna godiya ga manyan ‘yan kasuwa irin su Aliko Dangote, Abdul Samad Rabi’u, Muhammadu Indimi, Dahiru Mangal, Kola Adesina da Nasiru Danu.

Mamman Daura tare da mataimakin shugaban kasa
Mamman Daura tare da mataimakin shugaban kasa. Hoto: Kashim Shettima
Source: Twitter

Godiya ga jama’a baki daya

Yayin gode wa dukkan jama'ar da suka taya su alhini, Malam Mamman Daura ya ce:

“Mutane sun fito kwansu da kwarkwata wajen halartar jana’iza da addu’a ga Buhari. Muna matukar godiya da fatan Allah ya saka musu da alheri.”

Ya ce dangin suna jinjinawa jama’a daga dukkan matakai – gwamnati, jami’an tsaro, kungiyoyin al’umma, da kafafen yada labarai – bisa yadda suka nuna soyayya da mutuntawa ga marigayin.

Malam Mamman Daura ya yi godiya ga malaman addinin Musulunci da na Kirista da suka taya su alhini.

Kara karanta wannan

An gano bidiyon Aisha Buhari tana rusa kuka a gaban Shettima yayin da ya ke ta'aziyya

Jerin sunayen mutane 34 da dangin Buhari suka ambata:

1. Shugaba Bola Ahmed Tinubu

2. Uwargidansa, Sanata Remi Tinubu

3. Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima

4. Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda

5. Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum

6. Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar

7. Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Namadi Sambo

8. Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Farfesa Yemi Osinbajo

9. Babagana Kingibe

10. Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio

11. Shugaban Majalisar Wakilai, Hon. Tajuddeen Abbas

12. Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin

13. Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume

14. Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha

15. Shugaban Ma’aikata na yanzu, Hon. Femi Gbajabiamila

16. Tsohon Shugaban Ma’aikata, Farfesa Ibrahim Gambari

17. Tsohon Gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi

18. Sarkin Musulmi, Sultan na Sokoto

19. Shehun Borno

20. Sarkin Gwandu

21. Sarkin Katsina

22. Sarkin Daura

23. Alhaji Aliko Dangote

24. Abdul Samad Isyaka Rabi’u

25. Alhaji Muhammadu Indimi

26. Alhaji Dahiru Mangal

Kara karanta wannan

Mutanen Daura sun fadi yadda Buhari ya rayu a tsakaninsu bayan sauka a mulki

27. Kola Adesina

28. Nasiru Danu

29. Sarkin Ingila, Sarki Charles III

30. Sakataren Majalisar Dinkin Duniya

31. Mataimakiyar Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Amina Mohammed

32. Shugaban Kungiyar Tarayyar Afirka (AU)

33. Shugaban Kwamitin Shugabannin Kasashen ECOWAS

34. Tsohon Shugaban Kasa, Janar Abdulsalami Abubakar

An yi wa Buhari takwara a Bauchi

A wani rahoton, kun ji cewa wani matashi a jihar Bauchi, Malam Danladi Mai Kaset ya yi wa shugaba Muhammadu Buhari takwara.

Danladi Mai Kaset ya ce ya sanya wa dan shi suna Muhammadu Buhari ne saboda kyawawan halayen tsohon shugaban kasar.

Sheikh Isa Ali Pantami da ya yi aiki tare da shugana Buhari, ya ba matashin kyautar N200,000 domin sayen rago da hidimar suna.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng