2027: Sarkin Daura Ya Fadi Wanda Masarautar Za Ta Zaba a Gaban Matar Tinubu

2027: Sarkin Daura Ya Fadi Wanda Masarautar Za Ta Zaba a Gaban Matar Tinubu

  • Sarkin Daura ya karɓi baƙuncin uwargidan shugaban ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu yayin ta'aziyyar marigayi Muhammadu Buhari
  • Alhaji Umar Farouk Umar ya bayyana cewa Shugaba Tinubu ne zaɓin masarautar a zaɓen shekarar 2027 da ake tunkara
  • Mai martaba Sarkin ya bayyana cewa masarautar za ta ci gaba da marawa gwamnatin mai girma Bola Tinubu baya

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Katsina - Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Farouk Umar, ya yi magana kan Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Alhaji Umar Farouk Umar ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu shi ne ɗan takarar da masarautar Daura ke marawa baya domin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

Sarkin Daura ya yi magana kan zaben 2027
Sarkin Daura ya ce za su zabi Tinubu a 2027 Hoto: Daura Emirate Council Online, Sanusi Bature D-Tofa
Source: Facebook

Sarkin ya bayyana hakan ne a lokacin da yake karɓar baƙuncin uwargidan shugaban ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, a ranar Asabar, cewar rahoton jaridar Tribune.

Kara karanta wannan

Dantata: Gwamna Abba ya fadi abin da ke ransa kan ziyarar Tinubu zuwa Kano

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Uwargidan Tinubu ta je ta'aziyyar Buhari

Uwargidan shugaban ƙasan ta jagoranci wata tawaga ta manyan mata wajen kai ziyara ta jaje ga iyalan marigayi Shugaba Muhammadu Buhari a garin Daura, jihar Katsina.

Sanata Oluremi Tinubu tana tare da matan shugabannin majalisar tarayya, gwamnonin jihohi, ministoci, manyan hafsoshin tsaro da sauran fitattun mata.

A lokacin da suka kai ziyara ga Hajiya Aisha Buhari, matar marigayi shugaban ƙasa, tawagar ta yi addu’o’i domin Allah ya jikan marigayin, tare da ba iyalan da ya bari haƙurin rashi.

Sanata Tinubu da tawagarta sun ziyarci kabarin da aka binne tsohon shugaban ƙasa, inda aka gudanar da addu’o'i, kafin daga bisani su wuce gidan Alhaji Mamman Daura, ɗan uwan marigayi Shugaba Buhari kuma amintaccensa.

Uwargidan shugaban ƙasan ta bayyana marigayi Buhari a matsayin ɗan ƙasa nagari wanda ya ƙawata sunan iyalinsa, garinsa, jiharsa da kuma ƙasarsa.

A nasa martanin, Alhaji Mamman Daura ya nuna godiya bisa ziyarar uwargidan shugaban ƙasa, yana mai bayyana hakan a matsayin alamar girmamawa da ɗorewar zumunci.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu zai halarci taron addu'a da Allah Ya karɓi rayuwar Mai Martaba Sarki

Me Sarkin Daura ya ce kan 2027?

A fadarsa, Sarkin Daura ya karɓi gaisuwar jaje daga Oluremi Tinubu yana mai bayyana jimami da rashin ɗaya daga cikin fitattun ƴaƴan masarautar Daura.

Sarkin Daura na goyon bayan Tinubu
Sarkin Daura ya yabawa Bola Tinubu Hoto: Daura Emirate Council Online
Source: Facebook

A yayin nuna goyon baya, Sarkin ya yabawa jagorancin Shugaba Tinubu, tare da tabbatarwa Sanata Tinubu cewa masarautar Daura tana nan daram wajen marawa gwamnatinsa baya a 2027.

“Shugaba Tinubu shi ne zaɓinmu a 2027. Muna nan daram a bayansa, kuma za mu ci gaba da goyon bayan gwamnatinsa domin ta samu nasara."

- Alhaji Umar Farouk Umar

ADC ta caccaki Shugaba Tinubu

A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar haɗaka watau ADC ta caccaki shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan naɗe-naɗen muƙaman da ya yi.

ADC ta bayyana cewa Tinubu ya ba da muƙaman ne domin samun yardar mutanen Arewa waɗanda gwamnatinsa ta yi watsi da su.

Ta nuna cewa mutanen yankin ba za su bari a yaudare su ba domin sun san cewa an yi naɗe-naɗen ne ba da zuciya ɗaya ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng