Shugaba Tinubu Ya Dura Jihar Katsina ana Dakon Ƙarasowar Gawar Buhari

Shugaba Tinubu Ya Dura Jihar Katsina ana Dakon Ƙarasowar Gawar Buhari

  • Mai girma shugaban ƙasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Katsina yayin da ake shirye-shiryen jana'izar magabacinsa, Muhammadu Buhari
  • Gwamnan Katsina, Malam Dikko Raɗɗa da jami'an gwamnatinsa da takwarorinsa na wasu jihohi sun tarbi Bola Tinubu a filin jirgin sama
  • A halin yanzu dai ana dakon ƙarisowar tawagar mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, wanda ya ɗauko gawar Buhari daga Landan zuwa Katsina

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Katsina - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya isa jihar Katsina a wani bangare na shirye-shirye jana'izar marigayi tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari.

Ana sa ran Shugaba Tinubu da kansa ne zai karɓi gawar Buhari a Katsina domin girmamawa ta musamman gabanin a wuce da ita zuwa Daura.

Shugaba Tinubu.
Bola Ahmed Tinubu da muƙarrabansa sun isa Katsina Hoto: Ibrahima Kaulaha Muhammed
Source: Facebook

Masani kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a Najeriya, Zagazola Makama ya tabbatar da isowar Shugaba Tinubu a wani gajeren saƙo da ya wallafa a X.

Kara karanta wannan

Bidiyo: Yadda Gwamna Radda ya zubar da hawaye wajen birne Buhari a Daura

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tun jiya dai Bola Ahmed Tinubu ya turo ministoci da manyan kusoshin gwamnatinsa zuwa Daura domin tsara jana'izar ban girma ga Buhari.

Shirye-shiryen jana'izar Buhari sun kankama

Ƙarisowar Shugaba Tinubu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da ake dako domin shirin jana’izar ƙasa ta girmamawa da za a gudanar a Daura, garin da marigayin ya fito.

A Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Umaru Musa Yar’adua, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya tarbi Shugaban Tinubu tare da wasu manyan jami’an gwamnati da shugabannin siyasa.

Daga cikin waɗanda suka halarta domin tarbar shugaban ƙasa akwai Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Olufemi Oluyede, da Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Egbetokun.

Gwamnonin da suka je tarbar Shugaba Tinubu

Haka kuma wasu gwamnoni daga jihohin ƙasar nan sun je wurin tarbar Tinubu, ciki har da AbdulRahman AbdulRazaq na Kwara kuma shugaban ƙungiyar gwamnonin Najeriya (NGF).

Sauran gwamnonin sun haɗa da Mai Mala Buni na Yobe, Muhammadu Inuwa Yahaya na Gombe, Umar Namadi na Jigawa, Dr. Nasir Idris na Kebbi, da Dauda Lawal na Zamfara.

Kara karanta wannan

Duniya kenan: Yadda aka binne gawar Muhammadu Buhari a Daura

Yadda aka tarbi Shugaba Bola Tinubu a Katsina.
Shugaba Tinubu ya samu tarba mai kyau a jihar Katsina Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

Ahmed Aliyu na Sokoto, Babajide Sanwo-Olu na Legas, Dapo Abiodun na Ogun, Monday Okpebholo na Edo, Hope Uzodimma na Imo, da Bassey Edet Otu na Kuros Riba suna wurin.

Ana sa ran kowane lokaci gawar Buhari za ta ƙariso kuma Shugaba Tinubu zai karɓe ta, sannan ya yiwa wannan tawaga jagoranci zuwa Daura wurin birni marigayin.

Tinubu ya naɗa kwamitin jana'izar Buhari

A wani labarin, kun ji cewa Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya naɗa kwamitin ministoci da manyan jami'an gwamnti domin shirya jana'izar Muhammadu Buhari a Daura.

Tinubu ya ɗora wa kwamitin, wanda Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, zai jagoranta, alhakin tsarawa da gudanar da jana’izar da ta dace da darajar marigayi Buhari.

Kwamitin ya ƙunshi ministoci 10 da manyan jami'an gwamnatin Najeriya ciki har da mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu da wasu hadimai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262