An Ɗage Jana'izar Fitaccen Ɗan Kasuwa, Aminu Ɗantata saboda Ƴar Matsala a Madina

An Ɗage Jana'izar Fitaccen Ɗan Kasuwa, Aminu Ɗantata saboda Ƴar Matsala a Madina

  • An ɗaga jana'izar marigayi Alhaji Aminu Ɗantata zuwa ranar Talata, 1 ga watan Yuli, 2025 a ƙasar Saudiyya
  • Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama'a, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan bayan tawagar gwamnatin Najeriya ta isa Madina
  • Ya ce an samu wannan tsaiko ne sakamakon rashin isowar gawar marigayin a kan lokaci, wanda ya faru saboda ƙa'idojin da Saudiyya ta shimfiɗa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Saudi Arabia - Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta sanar da cewa an ɗage jana’izar fitaccen ɗan kasuwa kuma mai taimakon jama’a, Alhaji Aminu Dantata a Madina.

Kara karanta wannan

Zargin kisan kiristoci: Ɗan majalisar Amurka ya fashe da kuka yayin zama game da Najeriya

Aminu Ɗantata, ya rasu a ranar Asabar a Abu Dhabi, babban birnin Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE), bayan fama da jinya.

Marigayi Alhaji Aminu Dantata, dan asalin jihar Kano.
Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar Ɗantata zuwa gobe Talata Hoto: Bashir Ahmad
Source: Twitter

An ɗage jana'izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Ministan Yaɗa Labarai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan ga BBC Hausa, yana mai cewa an ɗaga jana'izar zuwa gobe Talata a Madina.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce akwai wasu ƙa’idoji da Saudiyya ta shimfiɗa dangane da shigar da gawa cikin ƙasar don yi mata jana’iza, wanda hakan ya kawo jinkirin kai gawar marigayin a kan lokaci.

Ministan ya tabbatar da cewa yanzu haka ana ci gaba da cike-ciken takardu tsakanin iyalan mamacin da hukumomin Saudiyya.

Abin da ya jawo jinkiri a jana'izar Ɗantata

“Da zarar an kammala cike-ciken, za a ɗauko gawar daga UAE zuwa Saudiyya,” in ji Muhammed Idris.

Ya ƙara da cewa ofishin Jakadancin Najeriya da ke Saudiyya da iyalan marigayin sun riga sun kammala duk wasu shirye-shiryen jana’iza, da zarar izini ya samu.

An ce Marigayi Aminu Dantata ya bar wasiyyar cewa a birne shi a Madina, birnin Manzon Allah (SAW), kuma Allah ya sa Saudiyya ta amince da hakan.

Kara karanta wannan

Ran maza ya baci: Tinubu ya umarci sojoji su ruguza 'yan ta'adda a Najeriya

Tuni dai tawagar Najeriya ƙarƙashin jagorancin Ministan Tsaro, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar, ta isa birnin Madina domin halartar jana’izar.

Za a yi jana'izar Ɗantata a gobe Talata.
Tawagar gwamnatin tarayya da ta Kano sun isa Saudiyya Hoto: Bashir Ahmad
Source: Facebook

Tawagar gwamnatin Najeriya ta isa Madina

Ƴan tawagar sun kunshi, Antoni Janar na ƙasa kuma ministan shari'a, Lateef Fagbemi (SAN), ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris da ƙaramin ministan harkokin gidaje, Yusuf Abdullahi Ata.

Haka kuma fitattun malaman addinin musulunci, Sheikh Aminu Daurawa, Dr Bashir Aliyu Umar, da Khalifa Abdullahi Muhammad na cikin tawagar.

Bugu da ƙari, Gwamna Abba Kabir Yusuf da takwaransa na jihar Jigawa, Umar Namadi sun jagoranci ta su tawagar domin halartar jana'izar Ɗantata a Madina

Daga cikin tawagar akwai Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, tsohon gwamnan Jigawa, Barista Ali Sa’ad Birnin Kudu, da wasu fitattun dattawan Kano.

Sakamakon tsaikon da aka samu wajen cika ƙa'idojin Saudiyya, an ɗaga jana'izar Ɗantata zuwa gobe Talata, kamar yadda Leadership ta rahoto.

Tinubu ya yi ta'aziyyar rasuwar Aminu Ɗantata

A wani labarin, kun ji cewa shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya yi alhinin rasuwar Alhaji Aminu Ɗantata, yana mai cewa wannan babban rashi ne ga ƙasa.

Kara karanta wannan

Trump: Gwamnati ta 'dora alhakin karuwar ta'addanci a Najeriya a kan shugaban Amurka

Tinubu ya yabawa gudummuwar da marigayin ya bayar wajen bunƙasa tattalin arzikin kasa da kuma taimakon jama'a.

Shugaban kasar ya ce Dantata ba wai kawai babban ɗan kasuwa ba ne, dattijo ne da ya kasance ginshikin zaman lafiya da cigaba a Najeriya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262