Sallah: Gwamnatin Kano Ta Hango Matsala, Ta Gargaɗi Musulmi kan Dabbobin Layya

Sallah: Gwamnatin Kano Ta Hango Matsala, Ta Gargaɗi Musulmi kan Dabbobin Layya

  • Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta ja hankalin mutanen jihar Kano kan dabbobin da za su yanka domin layya a lokacin babbar sallah
  • Kwamishinan lafiya na Kano, Abubakar Labaran ya bukaci jama'a su yi taka tsan-tsan, su tabbatar da lafiyar dabbobin da za su yanka
  • Ya taya ɗaukacin al'ummar musulmi na Kano murnar zagayowar sallah tare da fatan za su yi shagali cikin kwanciyar hankali da lumana

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta gargaɗi mutane game da dabbobin da za su yi layya da su a babbar sallah.

Gwamnatin ta bukaci mazauna jihar da su tabbata dabbobin da za su yanka a lokacin Sallar Layya mai zuwa lafiyayyu ne da za a iya ci.

Gwamnatin Kano ta buƙaci mutane su tsaftace naman layya da sallah.
Gwamnatin Abba ta gargaɗi mutanen Kano kan layya da dabbobi marasa lafiya Hoto: Getty Image
Source: Getty Images

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Lafiya, Nablusi Ahmad, ya fitar a ranar Laraba a Kano, kamar yadda Leadership ta rahoto.

Kara karanta wannan

Gwamna Bago ya bi sahun ƴan sandan Kano, ya hana hawan Sallah saboda abin da ya faru

Ya ce kwamishinan lafiya, Abubakar Labaran, ne ya yi wannan gargaɗin yayin da musulmai ke shirye-shiryen bukukuwan babbar sallah nan da ƴan kwanaki.

Gwamnatin Kano ta bada shawarar kula da lafiya

Kwamishinan ya ce hakan zai taimaka wajen kare lafiyar jama’a da kuma dakile yaduwar cututtukan da mutane ke iya ɗauka daga dabbobi.

Abubakar Labaran ya yi gargadi cewa akwai wasu cututtuka da ke iya yaduwa daga dabbobi zuwa mutane, musamman idan ba a dafa nama yadda ya kamata ba.

"Ya kamata mutane su ba da muhimmanci matuƙa wajen yadda ake dafa naman. Dafa shi sosai yana taimakawa wajen kashe ƙwayoyin cuta da ke tattare da dabbobin,” in ji shi.

An buƙaci ƴan Kano su tsaftace naman layya

Kwamishinan ya kuma bukaci iyaye mata da masu girki da su kula da tsaftar nama da kayan abinci yayin girki domin hana kamuwa da cututtuka.

Labaran ya shawarci jama’a da su wanke nama sosai da tsaftataccen ruwa kafin a dafa ko a adana shi.

Kara karanta wannan

Abba Kabir ya yi hadaka da tarayyar Turai domin kawo muhimman ayyuka Kano

Abubakar Labaran ya tabbatar da cewa gwamnati na da isassun magunguna da kayan agaji a cibiyoyin lafiya domin ba da kulawa cikin gaggawa idan an samu matsala.

Gwamnatin Kano ta ba mutane shawara kan dabbobin layya.
Gwamnatin Kano ta buƙaci jama'a su tabbatar da lafiyar dabbobin layya Hoto: Abba Kabir Yusuf
Source: Facebook

Ya kuma jaddada cewa ma’aikatar lafiyar ta jihar Kano ta kuduri aniyar ci gaba da kare lafiyar jama’a ta hanyar dakile yaduwar cututtuka, rahoton Guardian.

A karshe, kwamishinan ya taya jama’ar jihar Kano murnar zagayowar Sallah, tare da yi musu fatan za su gudanar da shagulgula cikin kwanciyar hankali, zaman lafiya da farin ciki.

'Yan sanda sun haramta hawan sallah a Kano

A wani rahoton, kun ji cewa Hukumar ‘Yan Sandan Kano ta sake jaddada haramcin gudanar da hawan Sallah a fadin jihar yayin bukukuwan babbar sallah.

Wannan mataki da ƴan sanda suka sake ɗauka ya saɓa wa mai martaba, Muhammadu Sanusi II, wanda ya fara shirye-shiryen hawan sallah.

Rundunar ƴan sanda ta taya musulmi da mazauna jihar Kano murnar zagayowar babbar Sallah, tare da kira da a kiyaye doka da oda.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262