Bawa: An Fara Jin Yadda Aka 'Sace' Kuɗin Tallafin Fetur, Tsohon Shugaban EFCC Ya Saki Littafi

Bawa: An Fara Jin Yadda Aka 'Sace' Kuɗin Tallafin Fetur, Tsohon Shugaban EFCC Ya Saki Littafi

  • Tsohon shugaban EFCC, Abdulrasheed Bawa ya rubuta littafi kan yadda aka wawure kuɗin tallafin man fetur a Najeriya
  • Bawa ya rike hukumar yaki da rashawa ta ƙasa watau EFCC daga watan Fabrairu, 2021 zuwa watan Yuni, 2023
  • Littafin dai ya tona asirin hanyoyin da jami'an gwamnati da ƴan kasuwa ke bi wajen wawure kuɗin tallafin mai a ƙasar nan

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Tsohon shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa (EFCC), Abdulrasheed Bawa, ya kaddamar da sabon littafi game da badaƙalar tallafin man fetur.

Littafin da Bawa ya rubuta ya yi bayani dalla-dalla kan yadda aka sace tare da wawure kudade da sunan tsarin tallafin man fetur a Najeriya.

Abdulrasheed Bawa zai saki littafin da ya rubuta.
Tsohon shugaban EFCC ya fitar da Littafi kan yadda aka wawure kudin tallafin man fetur Hoto: EFCC
Source: UGC

Jaridar The Cable ta tattaro cewa tsohon shugaban EFCC ya raɗawa littafin suna, “The Shadow of Loot & Losses: Uncovering Nigeria’s Petroleum Subsidy Fraud,” kuma ya kunshi batun tallafin mai.

Kara karanta wannan

Wike ya tono sirrin gwamnonin PDP, ya fadi alfarmar Tinubu da suke nema

Yaushe za a fitar da littafin tsohon shugaban EFCC?

Za a fitar da wannnan littafi a hukumance a ranar 5 ga Yuni, 2025, karkashin Cable Books, wani sashe a kamfanin Cable Media and Publishing Ltd.

Haka nan kuma za a rika sayar da littafin a fadin Najeriya ta hannun shagon sayar da litattafai na Roving Heights Bookstore.

Bawa ya rike kujerar shugaban EFCC daga Fabrairu 2021 zuwa Yuni 2023, lokacin mulkin tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, kamar yadda Guardian ta rahoto.

Kafin ya zama shugaban EFCC, Bawa ya kasance daya daga cikin manyan masu bincike a kwamitin musamman da EFCC ta kafa domin binciken badakalar tallafin man da ta kunno kai a shekarar 2012.

Abubuwan da littafin Abdulrasheed Bawa ya ƙunsa

A cikin littafin, Bawa ya bayyana yadda aka wawure biliyoyin Nairori ta hanyar dabaru da dama kamar:

  • Shigo da kaya na bogi
  • Karin kudin da babu cikakken bayani a kansu
  • Maimaita karbar tallafi
  • Canja takardun shigo da kaya
  • Safarar mai zuwa kasashen waje

Kara karanta wannan

Jirgin ruwa ya kife da mutane a tsakiyar kogi a Sokoto, an rasa rayuka

Littafin Abdulrasheed Bawa zai shiga kasuwa gobe Alhamis.
Tsohon shugaban EFCC, Bawa ya taɓo badakalar da manyan ƙasa ba su son a tona Hoto: @Naija_PR
Source: Twitter

Tsohon shugaban EFCC ya kara da cewa an yi amfani da waɗannan dabaru ne ta hanyar takardun bogi, rashin kulawa da haɗa baki tsakanin jami'an gwamnati da ƴan kasuwa.

Bawa ya tona yadda aka sace kudin tallafi

A cewarsa, littafin ba kawai tona badaƙalar cin hanci da rashawa kaɗai ya yi ba, ya ankarar da mahukunta domin daukar mataki da kuma riko da gaskiya a harkar tafiyar da kudaden jama’a a Najeriya.

A ranar 29 ga Mayu, 2023, lokacin rantsar da shi, Shugaba Bola Tinubu ya sanar da tuge tallafin man fetur.

Daga nan, farashin man fetur ya tashi daga N190 zuwa N500, har ya haura N1,000 kafin ya ɗan fara saukowa, wanda ya yanzu ake sayarwa kan N850 ko sama da haka.

EFCC ta yi nasiha da hadinin Manzon Allah SAW

A wani labarin, kun ji cewa hukumar EFCC ta yi jan hankali kan cin hanci da rashawa ta hanyar amfani da hadisin Manzon Allah (SAW).

Kara karanta wannan

Bayan karrama Bill Gates, an fadi yadda ya hada kai da Dangote ya ceci Arewa

EFCC ta yi amfani da hadisin Sahih Muslim wanda ya yi gargadi kan almundahana da kuma abin da zai biyo baya, idan shugaba ya wawuri dukiyar talakawa.

Hadisin ya gargadi shugabanni da su guji boye ko satar dukiyar jama'a, yana cewa za su zo da ita a ranar lahira duk yawanta.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262