Sanusi II Ya Bayyana Lokacin da Ya San Talauci a Rayuwarsa

Sanusi II Ya Bayyana Lokacin da Ya San Talauci a Rayuwarsa

  • Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya yi magana kan matsalar talaucin da ake fama da ita a Najeriya
  • Sanusi II ya bayyana mafi yawan manyan mutane da shugabanni ba su san ainihin menene talauci ba
  • Ya yi kiran da a tashi tsaye a haɗa kai don magance matsalar talauci da ta hana bayin Allah a ƙasar nan yin rayuwa mai inganci

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Sarkin Kano na 16 kuma tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Muhammadu Sanusi II, ya yi magana kan talaucin da ake fama da shi a Najeriya.

Muhammadu Sanusi II ya bayyana cewa ya fahimci ma’anar talauci ne kawai bayan ya hau karagar mulki a matsayin sarki.

Muhammadu Sanusi
Sanusi II ya koka kan talauci a Najeriya Hoto: Sanusi Lamido Sanusi
Source: Facebook

Sanusi II ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a wajen wani taro da aka gudanar don bikin zagayowar ranar haihuwar tsohon gwamnan jihar Rivers, Rotimi Amaechi na shekara 60, a birnin Abuja, cewar rahoton Vanguard.

Kara karanta wannan

Ambaliya: Sheikh Pantami ya yi magana kan mutuwar mutane sama da 100 a Jihar Neja

Sanusi II ya ce manyan mutane ba su san talauci ba

Sarkin na Kano na 16 ya bayyana cewa manya da yawa a ƙasar nan ba su san menene talauci ba, rahoton jaridar The Punch ya tabbatar.

“Yawancin manyan mutane a Najeriya ba su san ma’anar talauci ba. A matsayina na masanin tattalin arziƙi kuma tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, alƙaluma kawai na ke gani. Amma ban san talauci ba sai da na zama sarki."
“Idan ka tafi ƙauyuka ka ga irin ruwan da mutane ke sha, gidajen da suke ciki, azuzuwan karatu guda biyu marasa rufi."
“Shin muna ƙaunar mutane ne ko kuwa kawai muna ƙaunar mulkar su? Menene fifikonmu? Muna gina gadar sama da ƙasa a birane domin kanmu, alhali mutanen karkara ba za su iya isa asibiti ba."
"Muna cikin mawuyacin hali, abin da ya kamata mu mai da hankali a kai shi ne yadda za mu fita daga wannan matsala."

Kara karanta wannan

Musulmi sun yi babban rashi, Sarki mai martaba a Najeriya ya riga mu gidan gaskiya

Muhammadu Sanusi II

Sanusi II ya yi kira ga shugabanni da su kasance masu jin ƙai da nuna tausayi ga mutanen da aka damƙa musu jagoranci.

Muhammadu Sanusi II
Sanusi II ya halarci taron da aka shirya don Amaechi Hoto: Abba Attijjani
Source: Facebook

El-Rufai ya ce ana kuskure wajen yin zaɓe

A nasa jawabin, tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya nuna damuwa kan yadda ƴan Najeriya ke maimaita kuskure ta hanyar zaɓar baragurbin shugabanni.

“Muna ci gaba da zaɓar mutane da ba su da wata kwarewa face su ƙarbi mulki kawai, amma ba su san yadda za su gudanar da mulki ba."

- Nasir El-Rufai

Malami ya gargaɗi Sanusi II

A wani labarin kuma, kun ji cewa malamin addinin Kirista kuma shugaban cocin Evangelical Spiritual International, Primate Elijah Ayodele, ya ja kunnen Muhammadu Sanusi II.

Prinate Ayodele ya gargaɗi sarkin Kano na 16 kan ya bi sannu a hankali kuma ya yi taka tsan-tsan kan yadda yake gudanar da rayuwarsa.

Babban malamin addinin na Kirista ya ja kunnen Muhammasu Sanusi II kan ya sanya ido sosai kan irin abin da yake zuwa cikin cikinsa musamman abin da yake sha.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng