Babbar Sallah: Za a Raba Dubban Shanun Layya Kyauta ga Musulmi a Kano, Abuja da Jihohi 11

Babbar Sallah: Za a Raba Dubban Shanun Layya Kyauta ga Musulmi a Kano, Abuja da Jihohi 11

  • Wata gidauniyar Turkiyya (TDV) za ta yi layyar shanu 6,000 domin rabawa musulmi nama kyauta a jihohi 11 da birnin tarayya Abuja
  • Gidauniyar dai ta tsara rabawa talakawa, mabukata da masu ƙaramin karfi naman shanu 6,000 a lokacin shagalin babbar sallah
  • Wannan na zuwa ne bayan fadar mai alfarma Sarkin Musulmi ta sanar da ganin jinjirin watan babbar Sallah a daren ranar Talata

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Yayin da musulmi ke ci gaba da shirye-shiryen babbar sallah a makon gobe, wata gidauniya daga ƙasar Turkiyya za ta raba sadaƙar nama.

Gidauniyar mai suna, Turkiye Diyanet Foundation (TDV) ta kammala shirin layya da shanu 6,000 a jihohi 11 da kuma Babban Birnin Tarayya, Abuja.

Shanu.
Gidaunuyar Turkiyya za ta raba shanu 6,000 a lokacin babbar Sallah a Najeriya Hoto: Getty Image
Source: Getty Images

Jaridar The Nation ta tattaro cewa za a rabawa Musulmai marasa ƙarfi da masu buƙata naman waɗannan shanu 6,000 a lokacin bikin Sallar Layya (Eid al-Adha).

Kara karanta wannan

Tsadar rayuwa: An sanya ranar fara sabuwar zanga zangar adawa da mulkin Tinubu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sarkin Musulmi ya sanar da ganin wata

Wannan dai na zuwa ne bayan mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar na III ya tabbatar da ganin jinjirin watan Dhul Hijjah ranar Talata.

A sanarwar da fadar Sarkin Musulmi da ke Sakkwato ta fitar a daren Talata, Sultan ya ayyana ranar Laraba, 28 ga watan Mayu a matsayin 1 ga watan Dhul Hijjah, 1446H.

Hakan dai na nufin al'ummar musulmin Najeriya za su yi sallar idin layya ranar Juma'a, 10 ga watan Dhul Hijjah, 1446H wanda zai yi daidai da 6 ga watan Yuni, 2025.

Gidauniya za ta raba shanu a Abuja, jihohi 11

Bayan haka ne gidauniyar Turkiyya ta bayyana shirinta na yanka shanu 6,000 domin raba sadaƙar nama ga talakawa da mabukata a jihohi 11 da Abuja.

An ruwaito cewa za a raba naman shanun ne a cikin jihohin Bauchi, Oyo, Sokoto, Gombe, Kano, Nasarawa, Filato, Kaduna, Kogi, Niger, Jigawa da kuma FCT Abuja.

Kara karanta wannan

2027: Sanatoci sun gano dalilin kara karfin Boko Haram da sauran 'yan ta'adda

Wannan aikin layya yana daga cikin manya-manyan ayyukan jin ƙai da gidauniyar TDV ke yi da nufin rage yunwa da tallafa wa al’ummomin Musulmai.

Sallah.
Gidauniya za ta raba kyautar nama ga musulmi a Najeriya Hoto: Getty Image
Source: Getty Images

Taimakon da TDV take yi wa musulmai

Sauran ayyukan da gidauniyar ke gudanarwa sun haɗa da, gina masallatai, ciyar da masu azumi lokacin buɗa baki a watan Ramadan, d samar da ruwa mai tsafta ta hanyar haƙa rijiyoyi.

Sauran ayyaukan taimakon al'umma da gidauniyar ke yi sune, ba da tallafin karatu ga ɗalibai da kuma aikin tiyata kyauta ga marasa ƙarfi.

Wannan ya nuna cewa gidauniyar TDV na ci gaba da tallafawa al’ummar Musulmai a Najeriya, musamman a lokacin bukukuwa na ibada.

Talakawa sun sayawa gwamna ragon layya

A wani labarin, kun ji cewa mazauna unguwar Nayinawa a Gombe sun yi karo-karo, sun saya wa Gwamna Inuwa Yahaya ragon da zai yi layya da sallah.

Mutanen unguwar sun yi haka ne domin nuna godiya ga mai girma gwamnan bisa aikin cike wani kwari da ke hana shiga yankin, wanda aka kammala kwanan nan.

Kwarin da ke cikin unguwar Nayinawa ya kasance babban kalubale ga mazauna yankin, inda yake hana su zirga-zirga lokacin damina.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262