NEMA: Yadda Ɗan Ƙunar Baƙin Wake Ya Kusa Tada Bam a Barikin Sojoji a Abuja

NEMA: Yadda Ɗan Ƙunar Baƙin Wake Ya Kusa Tada Bam a Barikin Sojoji a Abuja

  • Hukumar NEMA ta tabbatar da fashewar bam din da ya auku a gaban barikin sojoji na Mogadishu, Abuja, a ranar Litinin da rana
  • Wani ɗan kunar bakin wake ya rasa ransa lokacin da bam ɗin da ke jikinsa ya tashi yayin yunƙurin shiga cikin barikin Mogadishu
  • An rahoto cewa jami’an tsaro daga sojoji, 'yan sanda, DSS, FRSC da kuma NEMA sun killace wajen da abin ya faru tare da yin bincike

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) ta bayyana cikakken bayani kan fashewar bam da ta auku a ranar Litinin, a babban birnin tarayya, Abuja.

Legit Hausa ta ruwaito cewa fashewar bam din ta auku ne a gaban shahararren barikin sojoji na Mogadishu da ke kan hanyar Abuja-Nyanya.

Kara karanta wannan

Tinubu zai kinkimo bashin dala biliyan 21.1 domin wasu ayyuka a Najeriya

NEMA ta yi magana kan bam din da ya tashi a kusa da barikin sojoji na Abuja
Jami'an hukumar NEMA sun isa inda bam ya tashi a kusa da barikin sojoji na Abuja. Hoto: @HQNigerianArmy, @nemanigeria
Source: Twitter

Bam ya tashi a kusa da sojoji a Abuja

Wasu ganau sun shaida wa jaridar Daily Trust cewa ana zargin wani ɗan kunar bakin wake da rasa ransa a lokacin da bam ɗin ya tashi.

Lamarin ya jefa jama’ar da ke wucewa a lokacin cikin firgici, inda mutane da dama suka watse domin neman tsira daga fashewar.

Rundunar ƴan sanda ta bayyana cewa sun fara gudanar da cikakken bincike, ciki har da tantance abubuwan fashewar ta hanyar binciken forensics.

A wata sanarwa da NEMA ta fitar ranar Talata, a shafinta na X, ta bayyana cewa fashewar ta auku ne yayin da wani ɗan ƙunar baƙin wake ya yi yunƙurin shiga cikin barikin sojojin Mogadishu.

NEMA ta ba da agaji bayan fashewar bam

Bam ɗin ya fashe a jikin mutumin yayin da yake ƙoƙarin shiga, wanda hakan ya yi sanadin mutuwarsa a wurin nan take, yayin da wani mai wucewa kusa da wurin ya jikkata.

Kara karanta wannan

An gano yadda dan kunar bakin wake ya so kutsawa barikin sojoji a Abuja

NEMA ta ce ta samu kiran gaggawa kan fashewar da misalin ƙarfe 1:47 na ranar Litinin, inda ta aika da tawagarta domin haɗa kai da jami’an tsaro wajen bada agaji.

Sanarwar ta ce:

"Da misalin ƙarfe 1:47 na ranar Litinin 26 ga Mayu, 2025, NEMA AOO ta samu kiran gaggawa game da fashewar bam a gaban barikin Abacha da ke kan titin Abuja-Keffi.
"Tawagar AYA ERAB ta shiga aiki nan da nan domin bada taimako, kuma ta iske har jami’an tsaro sun rufe wurin da abin ya faru domin ba da tsaro."
Hukumar NEMA ta tabbatar da mutuwar dan ƙunar baƙin wake da ya je tayar da bam a Abuja
Ofishin hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) da ke Abuja. Hoto: @nemanigeria
Source: UGC

'Dan ƙunar baƙin wake ya mutu nan take

Sanarwar ta ci gaba da cewa:

“Bayanan da aka tattara sun bayyana cewa wani ɗan kunar bakin wake ya yi yunkurin kutsawa cikin barikin sojojin, amma bam ɗin da ke jikinsa ya fashe.
"Fashewar ta yi sanadin mutuwar ɗan ƙunar baƙin waken nan take, yayin da wani da ke wucewa a wajen ya samu raunuka.
"Rundunar EOD ta ƴan sanda ta kai wanda ya jikkata asibitin kasa, sannan ta karɓi ikon gudanarwar wurin domin ci gaba da bincike. An kuma kammala aikin da misalin ƙarfe 5:29 na yamma."

Kara karanta wannan

Abu ya girma: 'Bam' ya tashi a kusa da sojoji a Abuja, mutane sun shiga fargaba

Sanarwar ta ce jami’an da suka halarci wurin da bam din ya tashi sun haɗa da NEMA, sojoji, 'yan sanda, DSS da kuma FRSC.

Ana zargin bam ya tashi a Abuja

A wani labarin, mun ruwaito cewa, wasu mazauna babban birnin tarayya, Abuja, sun shiga fargaba bayan wani abin fashewa da ake zargin bam ne ya tashi.

Shaidu sun bayyana cewa fashewar ta auku ne a ɗakin wasu maza biyu, inda aka fara zargin tukunyar gas ce ta fashe, amma babu tabbaci a kai.

Majiyoyi sun ce an sanar da ofishin ‘yan sanda faruwar lamarin, inda suka bukaci a kira ƙwararrun jami’an kwance bama-bamai domin tantance gaskiyar lamarin.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com