Mutuwa Ta Sake Girgiza Najeriya, Mai Magana da Yawun APC Ya Rasu a Ƙasar Waje

Mutuwa Ta Sake Girgiza Najeriya, Mai Magana da Yawun APC Ya Rasu a Ƙasar Waje

  • Mai magana da yawun jam'iyyar APC reshen jihar Ogun, Abdulraheem Tunde Oladunjoye ya rasu bayan fama da jinya a ƙasar waje
  • Iyalan marigayin sun tabbatar da rasuwarsa a wata sanarwa da suka fitar ranar Juma'a, sun ce za su sanar da lokacin da za a yi janaza
  • Gwamna Dapo Abiodun na jihar Ogun ya bayyana kaɗuwarsa bisa wannan rashi, yana mai cewa marigayin mutum ne mai kwazo da basira

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ogun - Sakataren yaɗa labarai na jam'iyyar APC reshen jihar Ogun, Alhaji Abdulraheem Tunde Oladunjoye, ya riga mu gidan gaskiya.

Marigayin, wanda ya kasance mai ba Gwamna Dapo Abiodun shawara kan harkokin yada labarai, ya rasu a ƙasar waje bayan fama da rashin lafiya da ba a bayyana ba.

Tunde Oladunjoye.
Mai magana da yawun jam’iyyar APC na Jihar Ogun, Tunde Oladunjoye, ya rasu Hoto: @OGSG_Official
Asali: Twitter

Kakakin jam'iyyar APC na jihar Ogun ya rasu

Kara karanta wannan

'Inyamurai sun rufe shaguna': Halin da ake ciki a Sokoto kan kisan Hausawa a Edo

Rahoton Daily Trust ya nuna cewa iyalan marigayi Tunde Oladunjoye sun tabbatar da rasuwarsa cikin wata sanarwa da suka fitar ranar Juma'a, inda suka ce:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Cikin bakin ciki da mika wuya ga Allah muna sanar da rasuwar mahaifinmu, mijinmu, ɗan’uwanmu kuma babban jagora, Alhaji Abdulraheem Olatunde Ayinde Oladunjoye, wanda ya rasu a ranar Juma’a, 4 ga Afrilu, 2025.
"Alhaji Oladunjoye mutum ne mai kima, gaskiya, da halin kirki. Rayuwarsa ta kasance cike da hidima da sadaukarwa ga jama’a.
"Bayan kasancewarsa uba nagari ga iyalinsa, ya zama uba ga da dama daga cikin al’umma. Ana girmama shi kuma an kaunace shi sosai da sosai."

- In ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa za a sanar da shirye-shiryen jana'izarsa (Janazah) nan ba da jimawa ba.

Gwamna Dapo Abiodun ya yi ta'aziyya

Gwamna Dapo Abiodun na jihar Ogun ya bayyana rasuwar Oladunjoye a matsayin babban rashi da ke da matuƙar wahalar jurewa.

Kara karanta wannan

Bayan rasuwar Sheikh Idris Dutsen Tanshi, Allah ya ɗauki rayuwar jigo a Najeriya

A cewarsa, ya girgiza da ya samu labarin rasuwar kakakin APC kuma hadiminsa, wanda ya ce ya kasance mutum mai kwazo da ƙarfin guiwa.

Gwamna Abiodun.
Gwamnan Ogun ya yi ta'aziyyar rasuwar kakakin APC Hoto: Prince Dapo Abiodun
Asali: Twitter
"Wannan labari na mutuwarsa ya girgiza ni matuƙa.Tunde mutum ne mai basira, ƙwazo da sadaukarwa wanda ya tsaya tsayin daka wajen kare manufofin gwamnati da jam’iyya.
"Ya kasance ɗaya daga cikin mutane mafi ƙwazo, mafi ƙarfin gwiwa, kuma mafi iya magana da jam’iyyar APC a Jihar Ogun ta taba samu a tarihi.
"Gaskiyarsa da rikon amana sun yi tasiri sosai wajen bunƙasa jam’iyyar APC a jihar. Oladunjoye mutum ne mai gaskiya, da tsantsar aminci. Zamu yi kewarsa ƙwarai."

- In ju Gwamna Dapo Abuodun.

Jigon PDP a jihar Oyo ya kwanta dama

A wani labarin, kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar PDP (na Kudu), Yekini Ayoade Adeojo, ya riga mu gidan gaskiya.

An ruwaito cewa jigon jam'iyyar PDP ya rasu ne ranar Juma'a, 4 ga watan Afrilu, 2025 a gidansa da ke Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

A 1999, Adeojo ya nemi takarar gwamna a ƙarƙashin PDP, amma ya sha kaye a hannun marigayi Alhaji Lamidi Adesina na jam’iyyar AD.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng

iiq_pixel