Malamin Musulunci Ya Fanɗarewa Sarkin Musulmi, Ya Fadi Ranar Sallar Idi a Najeriya

Malamin Musulunci Ya Fanɗarewa Sarkin Musulmi, Ya Fadi Ranar Sallar Idi a Najeriya

  • Sheikh Muhammed Habibullah Adam Abdullah El-Ilory ya bayyana Litinin, 31 ga Maris, 2025, a matsayin ranar Eid-el-Fitr a Najeriya, bisa ga ka’idojin ilimi da addini
  • Malamin ya ce ba za a iya ganin sabon jinjirin wata ba a ranar 29 ga Maris, 2025, don haka 31 ga Maris ita ce ranar farko ta Shawwal
  • Sheikh El-Ilory ya jaddada cewa ilimin taurari na zamani na iya hango lokaci da matsayin wata, kamar yadda ake hasashen faduwar rana da duniyar rana
  • Ya bukaci Musulmai su hada ilimi da koyarwar addini wajen tantance ranar Sallah, tare da mika fatan alheri ga jagororin Musulunci a Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Agege, Lagos - Sheikh Muhammed Habibullah Adam Abdullah El-Ilory ya fadi ranar da za a sallar Idi a Najeriya.

Kara karanta wannan

Hafsan tsaro ya tsoma baki kan kisan ƴan Arewa a Edo, ya fadi shirinsu kan lamarin

Shehin malamin ya bayyana Litinin, 31 ga Maris, 2025, a matsayin ranar Eid-el-Fitr ga Musulmin Najeriya, bisa ka'idojin kimiyya da addini.

Malamin Musulunci ya fadi ranar idi saɓanin Sarkin Musulmi
Malamin Musulunci ya barranta da Sarkin Musulmi, ya ce ranar Litinin ce sallah. Hoto: @Habibelilory.
Asali: Twitter

Sallah: Malami ya saba da Sarkin Musulmi

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Nurudeen Ibrahim, ya wallafa a shafin Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sheikh El-Ilory ya bayyana cewa kimiyyar taurari na zamani na iya tantance bayyanar sabon wata.

Malamin ya bayyana cewa:

"Da taimakon fasahar zamani, ana iya sanin lokaci da wuri na bayyanar wata, kamar yadda ake hasashen fitowar rana da duniyar rana."

Ya ce a ranar 29 ga Maris, 2025, shekarun sabon wata a Najeriya zai kasance awanni 6 da mintuna 59, wanda ba zai ba da damar ganin jinjirin da ido ba.

Haka nan, a Saudiyya, shekarun jinjirin zai kasance awanni 4 da mintuna 40, wanda hakan na nufin ba za a iya ganinsa da ido ba.

Kara karanta wannan

Bayan Saudiyya, Sarkin Musulmi ya sanar da ranar karamar Sallah a Najeriya

Ya kara da cewa:

"Samuwar hoton da manhajojin CCD ke samarwa ba ya cikin Sunnah na Manzon Allah (SAW), kamar yadda koyarwar addini ta bayyana."
"Litinin, 31 ga Maris, ita ce 1 ga Shawwal, kuma ranar Eid-el-Fitr bisa ga koyarwar Annabi da kimiyyar zamani."
"Allah ya kawo mana zaman lafiya da albarka a wannan bikin Eid-el-Fitr."
Shehin malami ya saba da Sarkin Musulmi kan sallar idi
Malamin Musulunci ya ce ranar Litinin za a sallah karama. Hoto: @Habibelilory.
Asali: Twitter

Malami ya shawarci Musulmi kan haɗin kai

Sheikh El-Ilory ya bukaci Musulmai su hada ilimi da addini don gujewa rudani kan ranar Sallah a Najeriya.

Ya mika fatan alheri ga jagororin Musulunci a Najeriya, ciki har da Mai Martaba Sultan, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar.

Har ila yau, malamin ya yi addu'ar gudanar da bukukuwan sallah cikin aminci da walwala a Najeriya ba tare da tsaiko ba.

Sarkin Musulmi ya sanar da ganin wata

A baya, mun ba ku labarin cewa Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar ya fitar da sanarwa kan ganin watan Shawwal a Najeriya.

Kara karanta wannan

Rai baƙon duniya: Musulunci ya yi rashi bayan sanar da rasuwar malami a watan azumi

Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar ya bayyana an samu rahotannin ganin watan Shawwal 1446AH a sassa daban-daban na Najeriya.

Sultan ya bayyana cewa yau Lahadi, 30 ga watan Maris 2025, ita ce daidai da 1 ga watan Shawwal 1446AH.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng