Rikicin Rivers: Jerin Gwamnonin da Suka Goyi Bayan Tinubu a Dakatar da Fubara
Jihar Rivers - Rikicin siyasa da ke addabar jihar Rivers ya tsananta, inda har ƴan majalisar dokokin jihar suka yi barazanar tsige Gwamna Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Bayan rikicin ya ƙi ci ya ƙi cinyewa, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta ɓaci a jihar mai arziƙin mai.

Asali: Twitter
Shugaban ƙasa ya dakatar da gwamnatin jiha
Shugaban ƙasan ya sanar da sanya dokar ta ɓacin ne a wani jawabi da ya yi wa ƴan Najeriya, wanda hadiminsa Dada Olusegun ya sanya a shafinsa na X.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Mai girma Bola Tinubu ya kuma dakatar da Gwamna Fubara, mataimakiyarsa da ƴan majalisar dokokin jihar har na tsawon watanni shida.
Shugaban ƙasan ya kuma naɗa Vice Admiral Ibok-Ete Ekwe Ibas (mai ritaya) a matsayin shugaban riƙo wanda zai ci gaba da jan ragamar harkokin mulki a jihar har na tsawon watanni shida.

Kara karanta wannan
Sanatan Bauchi ya ba mutane kunya da azumi, bidiyosa yana rabon kuɗi ya shiga intanet
Wannan mataki na Tinubu ya jawo cece-kuce a tsakanin ƴan Najeriya daga fannoni daban-daban, inda aka samu masu nuna goyon baya da masu akasin haka.
Rikicin Rivers ya ƙi ci ya ƙi cinyewa
Rikicin siyasar Rivers ya fara ne kimanin wata shida bayan Simi Fubara ya kama aiki a matsayin gwamna, inda ake zarginsa da yunƙurin tsige kakakin majalisar dokokin jihar, cewar rahoton Businessday.
Wannan yunƙurin da Gwamna Fubara ya yi bai yi wa tsohon gwamnan jihar Rivers, Nyesom Ezenwo Wike, daɗi ba.
Wike, wanda a halin yanzu ke matsayin ministan babban birnin tarayya Abuja, ya zargi Fubara da ƙoƙarin ƙwace tsarin siyasar jihar daga hannunsa.
Fubara a na sa ɓangaren ya yi zargin cewa tsohon gwamnan ya ƙi sakar masa mara wajen gudanar da harkokin mulkin jihar.
Duk da ƙoƙarin shiga tsakani da aka yi, rikicin ya ƙi warwaruwa cikin lalama, lamarin da har sai da ya kai zuwa ga kotuna.
Gwamnonin da suka goyi bayan matakin Tinubu
Duk da sukar da wasu ke yi, akalla wasu gwamnoni guda uku sun goyi bayan matakin da shugaban ƙasan ya ɗauka kan rikicin siyasar jihar Rivers.
Dukkanin gwamnonin dai na jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ne kuma sun fito ne daga yankin Kudancin ƙasar nan.
Ga jerinsu a nan ƙasa:
1. Hope Uzodimma na Imo

Asali: Facebook
Gwamnan jihar Imo, wanda kuma shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin jam'iyyar APC, Hope Uzodimma, ya bayyana goyon bayansa kan sanya dokar ta ɓaci da Shugaba Tinubu ya yi a jihar Rivers.
A wani taron manema labarai, Uzodimma ya ce matakin da Tinubu ya ɗauka ya yi daidai domin kawo ƙarshen rikicin siyasar da ke ƙara ta'azzara a jihar mai arziƙin mai.
Ya ƙara da cewa, rikicin siyasar Rivers na iya dagula jihar da ma tattalin arziƙin Najeriya baki ɗaya.
Kalli bidiyon jawabinsa a nan:
2. Monday Okpebholo na Edo

Asali: Twitter
Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo, ya yabawa Shugaba Tinubu bisa ayyana dokar ta-ɓaci a Rivers, inda ya bayyana cewa matakin ya ceto tattalin arziƙin ƙasar nan.
A cewar jaridar The Nation, Okpebholo, yayin da yake wakiltar Tinubu a bikin ƙaddamar da aikin titin tarayya a Edo, ya soki tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan, wanda ya ce matakin zai zubar da mutuncin Najeriya a idon duniya.
Okpebholo ya bayyana cewa tsohon shugaban ƙasan bai iya ɗaukar matakan da suka dace ba lokacin da yake mulki, shiyasa yake sukar Shugaba Tinubu.
Ya ce matakin da shugaban ƙasan ya ɗauka ya yi daidai domin dawo da zaman lafiya a yankin Neja Delta.
3. Gwamnan rikon kwarya a Cross River
Gwamnatin Jihar Cross River ta nesanta kanta daga matsayar Kungiyar gwamnonin Kudu maso Kudu, wadda ta nuna rashin amincewa da ayyana dokar ta ɓaci a Rivers.
A cewar jaridar Leadership, muƙaddashin gwamnan jihar Cross River, Peter Odey, ya bayyana cewa jiharsa na goyon bayan matakin Tinubu, domin dawo da doka da oda da kuma dakile rikicin da ke ƙara dagulewa a jihar Rivers.
SERAP ta kai Tinuubu ƙara kotu
A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙungiyar SERAP ta ɗauki matakin shari'a kan ayyana dokar ta ɓaci da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi a jihar Rivers.
SERAP ta ƙalubalanci matakin dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara da sauran zaɓaɓɓun jami'an gwamnati da Shugaba Tinubu ya yi.
A ƙarar da ƙungiyar ta shigar a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci kotun da ta ba da umarnin soke dakatarwar da aka yi wa Gwamna Fubara.
Asali: Legit.ng