'Dan Shugaban Kasa, Seyi Tinubu Ya Gamu da Fushin Matasa, an Dakawa Motar Tallafinsa Wawa

'Dan Shugaban Kasa, Seyi Tinubu Ya Gamu da Fushin Matasa, an Dakawa Motar Tallafinsa Wawa

  • Matasa sun farwa motar abinci da ake zargin ta ɗauko tallafin da ɗan shugaban ƙasa, Seyi Tinubu zai rabawa jama'a a jihar Gimbe
  • Rahotanni sun bayyana cewa matasan sun dakawa motar wawa, suka kwashe kayan da suka haɗa da shinƙafa, sukari da sauransu
  • Tsohon dan takarar kujerar Majalisa a Kano, Hon. Adnan Mukhtar TudunWada ya ce abin da Seyi ke yi cin mutunci ne ga 'Yan Arewa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Gombe - Fustattun matasa sun daka wawa kan motar da ta ɗauko kayan abinci da ake zargin ɗan shugaban ƙasa, Seyi Tinubu ya aika jihar Gombe.

Idan ba ku manta ba Seyi Tinubu ya ziyarci jihohin Arewa da dama, inda yake buɗa baki da jama'a da shugabannin siyasa.

Seyi Tinubu.
Matasa sun fasa motar tallafin azumin Ramadan da Seyi Tinubu ya aika Gombe Hoto: Seyi Tinubu
Asali: Facebook

Ziyarce-ziyarcen Seyi Tinubu a Arewa

A yayin wadannan ziyarce-ziyarce, yakan kaddamar da shirin bayar da tallafin abinci ga marasa galihu a lokacin Ramadan, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Kara karanta wannan

An ba Kwankwaso shawara kan shirin haɗakar Atiku, Peter Obi da El Rufai a 2027

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wasu na yabawa da shirin, yayin da wasu ke sukarsa, suna masu cewa yankin Arewa ya cancanci samun wani tsare-tsaren ci gaba maimakon tallafin abinci kawai.

Ɗan gwamnan Bauchi ya yi magana

Shamsuddeen Bala Mohammed, ɗan gwamnan jihar Bauchi, ya soki wannan shiri na Seyi, yana mai bukatar a samar da wani shirin ci gaban matasa mai dorewa.

Ya ce:

"Dan Allah, idan ka zo Bauchi, muna bukatar ka ba matasa ayyukan yi, Keke Nafef, kudin fara kasuwanci, cibiyoyin fasaha, da horo kan kasuwancin crypto."
"Matasan Bauchi ba sa bukatar shinkafa da abinci cikin leda a lokacin Ramadan. Su ba mabarata ba ne."

Matasa sun dakawa motar abinci wawa

Duk da cewa Seyi bai kai ziyara zuwa wasu jihohin Arewacin Najeriya ba tukuna, rahotanni sun nuna cewa kayan tallafinsa sun isa Jihar Gombe.

A wani bidiyo da wata jarida ta wallafa, an ga wasu matasa suna kwasar kwalayen kayan abinci daga wata mota da aka ajiye a gefen hanya.

Kara karanta wannan

Sanata Kalu ya watsa wa matasan Arewa ƙasa a ido, ya yi maganar karawa da Tinubu a 2027

An hango matasan sun shiga cikin motar, suna jefo kayan abincin da suka haɗa da shinkafa, sukari, man girki, gishiri, da taliya ga jama’a da ke kasa, su kuma su tsere da su.

Rahotanni sun ce an tura tireloli guda biyu dauke da kwalaye 3,500 na kayan abinci zuwa Gombe.

Ɗaya daga cikin motocin an raba kayan lafiya, yayin da ta biyun kuma ta gamu da fushin matasa, waɗanda suka wawashe kayan ciki gaba ɗaya.

Duk da cewa Seyi ya bayyana wannan shiri nasa a matsayin "Rangadin Ramadan" da shirin jawo matasa a jiki wasu masu fashin baki na ganin hakan a matsayin wata dabara ta siyasa.

Seyi Tinubu.
Matasa sun wawashe kayan abincin da ake zargin na Seyi Tinubu ne Hoto: Seyi Tinubu
Asali: Twitter

Seyi Tinubu na cin mutuncin Arewa

A wata hira da Legit Hausa ta wayar tarho, tsohon ɗan takarar Majalisar Dokokin Kano, Hon. Adnan Muktar TudunWada, ya soki ziyarce-ziyarcen Seyi Tinubu a Arewa.

A cewarsa, Arewa ta fi bukatar a bunƙasa harkokin ilimi, samar da cibiyoyin fasahar zamani, ƙarin jami'o'i da sauran ayyukam ci gaba fiye da rabon abinci.

Kara karanta wannan

Gwamna Abba ya yi buda biki da marayu, ya ɗauki alkawarin ba su aikin yi

A kalamansa ya ce:

"Ba abinci matasan Arewa ke buƙata ba, muna bukatar inganta ilimi, samar da cibiyoyin fasaha, karin makarantu da sauran ababen more rayuwa.
"Abin da Seyi ke yi a fadar sarakunan Arewa cin mutunci ne, bai isa ya yi haka a idan ya je wurin sarakunan yarbawa ba."

Bola Tinubu ya ba ƴan APC buhunan shinkafa

A wani labarin, kun ji cewa Bola Tinubu ya aika gudunmawar buhunan shinkafa 7,000 a matsayin tallafin Ramadan ga ƴaƴan jam’iyyar APC a jihar Zamfara.

Ƙaramin ministan tsaro kuma tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle ya kaddamar da rabon tallafin a ranar Juma’a da ta gabata.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262