Masu Safarar Yara Sun Yiwa 'Yan Sandan Najeriya Tayin Cin Hancin Naira Miliyan 1

Masu Safarar Yara Sun Yiwa 'Yan Sandan Najeriya Tayin Cin Hancin Naira Miliyan 1

  • Rundunar ‘yan sandan Imo ta cafke mutum biyu da ake zargi da safarar yara tare da ceto yara biyu da aka sace a wurare daban-daban
  • Kakakin rundunar, Henry Okoye, ya ce jami’an sun nuna kwarewa wajen kin karbar cin hancin Naira miliyan daya domin tabbatar da adalci
  • An ceto yaran da aka sace, kuma bincike ya nuna akwai babbar cibiyar safarar yara da ake kokarin bankadowa yanzu haka a jihar Imo

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Imo - Rundunar ‘yan sandan jihar Imo ta cafke wasu mutum biyu da ake zargi da safarar yara, tare da ceto yara biyu da aka sace a wurare daban-daban.

Kakakin rundunar, Henry Okoye, ya bayyana cewa jami’an ‘yan sanda sun nuna kwarewa wajen kin karbar cin hancin Naira miliyan daya domin tabbatar da adalci.

Kara karanta wannan

'Yan sanda sun kai farmaki zazzafa, sun kama 'yan fashi 35 masu tare hanyoyi

Rundunar 'yan sandan Najeriya ta yi magana da ta samu tayin N1m daga masu safarar mutane
'Yan sandan Najeriya sun ki karbar tayin N1m daga masu safarar mutane a Imo. Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

'Yan sanda sun ki karbar cin hancin N1m

Jaridar Vanguard ta rahoto Henry Okoye yana cewar, jami’an rundunar da ke gudanar da bincike a titin Owerri-Aba suka kama wata mata mai suna Eze Chika, mai shekaru 45.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Okoye ya ce, a binciken 'yan sandan na ranar 21 ga Fabrairu, an samu matar da wani yaro dan shekara hudu da aka sato, amma a farko ta yi ikirarin cewa dan nata ne.

Daga baya, ta amsa cewa ta sayi yaron daga wajen wata kungiya da ake zargin ta masu safarar yara ce a garin Aba, a kan kudi Naira miliyan 1.8.

Da take kokarin tserewa daga hukunci, matar ta yi yunkurin ba wa jami’an ‘yan sanda cin hanci na Naira miliyan daya, amma suka ki karba.

Jami’an sun cafketa tare da ceto yaron cikin koshin lafiya, kuma bincike ya nuna tana da alaka da wata babbar cibiyar safarar yara.

An kama matar da ta sace yaron makociyarta

Kara karanta wannan

APC ta fadi abin da zai mayar da Tinubu kujerarsa bayan zaben 2027

A wata sabuwar nasara, jami’an SCID sun kama wata mata mai suna Confidence Odo, mai shekaru 32, bisa zargin sace yaron tsohuwar makwabciyarta.

Rundunar 'yan sanda ta kubutar da yaran da aka sace a Imo
'Yan sanda sun nuna kokari bayan sun kubutar da yara 2 da aka sace a Imo. Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

Rahotanni sun bayyana cewa Odoh ta saci yaron ne a ranar 4 ga Fabrairu, yayin da yake wasa a harabar gidansu.

An ceto yaron kuma aka mayar da shi hannun iyayensa, Mista da Misis Michael Ududiri, yayin da ake ci gaba da farautar masu hannu a satar.

'Yan sanda sun ba da lambar tuntuba

Kakakin ‘yan sandan ya jaddada aniyar rundunar wajen yaki da safarar yara da sauran manyan laifuka a jihar Imo.

Ya bukaci iyaye su kasance masu lura da ‘ya’yansu tare da hana su yawo ba tare da wani sa ido ba.

Rundunar ta kuma bukaci al’umma su rika kai rahoton duk wani motsi da suke zargin na masu safarar yara ne zuwa ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

Domin bayar da rahoto kai tsaye, rundunar 'yan sandan ta bayar da lambobin kira kamar haka: 08034773600 da 08148024755.

Kara karanta wannan

'Yan sanda sun ritsa 'yan bindiga a maboyarsu, an kama 'yan ta'adda 20

'Yan sanda sun ki karbar cin hancin N174m

A wani labarin, mun ruwaito cewa, jami’an ‘yan sandan Najeriya na reshen Legas sun bayyana cewa sun ki karbar cin hanci daga wani dan damfara, Patrick Akpoguma.

A cewar rundunar, wanda ake zargin, wanda ke damfarar mutane ta yanar gizo, ya yi kokarin ba su rashawa har Naira miliyan 174 domin kaucewa hukunci.

An ce Akpoguma ya shahara wajen yaudarar mutane ta hanyar soyayya, satar kudi, da tsafi ta yanar gizo, lamarin da ya sa yake kokarin kubuta daga hannun ‘yan sanda.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.