Shugaban EFCC Ya Fallasa 'Yan Siyasa da Suka ba Shi Cin Hancin N500m

Shugaban EFCC Ya Fallasa 'Yan Siyasa da Suka ba Shi Cin Hancin N500m

  • Shugaban EFCC, Olanipekun Olukoyede ya yi tone-tone kan yadda cin hanci ke kara yawa a Najeriya
  • Olukoyede ya fadi yadda ya ƙi karɓar N500m da aka ba shi a lokacin jana’izar mahaifiyarsa a jihar Ekiti a 2019
  • Ya bayyana cewa mutane da dama, ciki har da ministoci da shugabannin hukumomi, sun aiko masa da kuɗi da kyaututtuka, amma ya mayar da su
  • Shugaban EFCC ya ce ya guji karɓar kuɗin ne don guje wa abin da ka iya zamar masa tarnaki a aikinsa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

FCT, Abuja Shugaban Hukumar EFCC, Olanipekun Olukoyede ya bayyana yadda ya tsallake karbar cin hanci daga yan siyasa.

Olukoyede ya ce ya ƙi karɓar fiye da N500m da aka ba shi a lokacin rasuwar mahaifiyarsa a jihar Ekiti.

Kara karanta wannan

Shugaban EFCC ya yi hangen nesa, ya fadi dalilin karuwar cin hanci a Najeriya

Shugaban EFCC ya koka yadda cin hanci ke kara yawa a Najeriya
Shugaban EFCC ya bayyana yadda aka kawo masa cin hancin fiye da N500m. Hoto: Economic and Financial Crimes Commission.
Source: Facebook

Yadda shugaban EFCC ya ki karbar cin hanci

Olukoyede ya bayyana hakan ne a taron ACSR karo na 38 da aka gudanar a Abuja, cewar Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban EFCC ya bayyana yadda ya tsallake tarnaki game da cin hanci da aka kawo masa tun a wancan lokaci.

A cewarsa:

"Na rasa mahaifiyata a 2019 a jihar Ekiti, mun je jana’iza ni ne Sakataren EFCC ne a lokacin.
"Ranar jana’iza, na zo gida sai na tarar da shanu 17 a harabar gidana, a cikin su har da masu ciki.
"Da na isa gida, maigadi na ya kawo mini wata karamar akwati a ciki kuwa sai na ga takardun biyan kudi daga banki da yawa daga jami’an gwamnati."
"Na kai su duka ga matata, ta ce, ‘Alhamdulillah.’ na ce, ‘Alhamdulillah don me?’ da muka ƙirga su, sun kai kusan N500m."
Shugaban ya fadi yadda ya ki amincewa da karbar cin hancin N500m

Source: Facebook

Olukoyede ya gargadi masu aiko masa cin hanci

Kara karanta wannan

'Tsufa ke damunka': NNPP ta dura kan Ganduje da ya ce zai raba Abba da kujerarsa

Olukoyede ya ce ya tattara duk takardun inda ya rubuta wasiƙa ga masu aikowa, sannan ya mayar da su don guje wa duk wata matsala a gaba.

Ya kara da cewa:

"An yi jana’izar a watan Satumba 2019, amma zuwa watan Yulin 2020, an bincike ni, idan na karɓi waɗannan kuɗin, me zan ce?"
"Da an ce na karɓi kuɗin ne don jana’izar mahaifiyata, amma wasu daga cikin masu bayarwa na cikin binciken EFCC."

Olukoyede ya ce da ɗan’uwan matarsa ya ji abin da ya yi, ya bar yi masa magana na tsawon wasu watanni shida, Daily Trust ta ruwaito.

Ya ce da har an samu wadannan kudi a bankinsa, da shi ma zai iya tsintar kansa a gidan yari a yanzu.

EFCC sun mamaye ofishin hukumar NAHCON

Kun ji cewa Jami'an hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC, sun yi dirar mikiya a hedkwatar hukumar Alhazai ta ƙasa (NAHCON) da ke Abuja.

An ce lokacin samamen da jami'an EFCC suka kai, sun tsare kakakin hukumar NAHCON tare da wasu mutane uku domin gudanar da bincike.

Kara karanta wannan

An yanke makomar Ganduje, APC ta bayyana yankin da ta maida shugabancin jam'iyya

Rahotanni sun ce jami'an sun kai samamen ne a binciken da suke ci gaba da yi kan zargin karkatar da tallafin N90bn da aka ba da a lokacin aikin Hajjin 2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.