Tashin Hankali: An Janye Dukkanin Jami'an Tsaron da ke Gadin Kakakin Majalisa

Tashin Hankali: An Janye Dukkanin Jami'an Tsaron da ke Gadin Kakakin Majalisa

  • An janye dukkanin jami’an tsaron da ke kula da shugabar majalisar jihar Legas, Mojisola Meranda, lamarin da ke barazana ga tsaronta
  • Wani hadimin Rt. Hon. Mojisola Meranda ya bayyana cewa an janye dukkanin jami'an tsaron da suka hada da 'yan sanda da na DSS
  • Wannan na zuwa ne yayin da magatakardar majalisar da aka tsige yayi yunkurin komawa ofishinsa, lamarin da ya jawo hatsaniya a ranar

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Legas - Rikicin da ke gudana a majalisar jihar Legas ya dauki sabon salo bayan an janye dukkanin jami’an tsaron da ke gadin shugabar majalisar, Mojisola Meranda.

Wannan ci gaban ya zo ne a daidai lokacin da ake fama da rikicin shugabanci a majalisar, lamarin da ke barazanar kawo rashin tsaro ga kakakin majalisar.

Rikicin majalisar Legas ya dauki zafi da aka janye jami'an tsaron shugabar majalisar
An janye dukkanin jami'an tsaron da ke gadin Mojisola Meranda, shugabar majalisar Legas. Hoto: @lshaofficial
Asali: Twitter

An bar shugabar majalisa babu tsaro

Kara karanta wannan

Bayan kalaman El Rufai, Tinubu, Shettima, Ganduje sun kira taron kusoshin APC a Abuja

Wani hadimin shugabar majalisar, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya tabbatar wa jaridar Vanguard cewa an janye jami’an tsaron da suka hada da ‘yan sanda da DSS da safiyar Alhamis.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hadimin ya ce:

"A safiyar Alhamis muka tashi da abin mamaki, domin mun gano cewa an janye dukkanin jami’an tsaron da ke kula da kakakin majalisa, Mojisola Meranda.
"Wannan ya hada da ‘yan sanda da DSS, lamarin da zai jefa ta a rashin tsaro, musamman a wannan lokaci na rikicin shugabanci."

Punch ta ruwaito hadimin ya bukaci Gwamna Babajide Sanwo-Olu da ya hanzarta daukar matakin da ya dace domin hana barkewar rikici a majalisar.

An hana tsohon magatakardan majalisa shiga ofis

Wannan na zuwa yayin da a ranar Laraba, Olalekan Onafeko, tsohon magatakardan majalisar da aka dakatar, ya yi kokarin komawa ofishinsa.

Hadimin shugabar majalisar Legas ya magantu da aka janyewa Merinda jami'an tsaro
An janye jami'an tsaron da ke gadin shugabar majalisar Legas a ranar Alhamis. Hoto: @lshaofficial
Asali: Twitter

Sai dai, jami’an tsaro sun dakatar da shi cikin lumana tare da hana shi shiga harabar majalisar.

Kara karanta wannan

Jerin Majalisun dokoki na jihohi 6 da aka sha fama da rikicin shugabanci a Najeriya

An ruwaito cewa Onafeko, wanda aka cire tare da tsohon shugaban majalisar, Mudashiru Obasa, ya iso harabar majalisar da karfe 9:00 na safe, tare da lauyansa, jami’an tsaro biyu da wasu jami’an DSS.

"An shawarci magatakardar da aka dakatar da ya fice cikin lumana daga harabar majalisar, tun da dai ana sauraron karar da ke gaban kotu," in ji wani ganau.

Ma'aikatan majalisar Legas sun yi Allah-wadai

A wani faifan bidiyo da ke ta yawo a kafafen sada zumunta, an hangi ma’aikatan majalisar suna yi wa Onafeko ihun rashin amincewa yayin da ake korar sa daga harabar majalisar.

Biyo bayan lamarin, majalisar Legas, ta hannun babban jami'in tsaron majalisar, Kushoro Idowu ta fitar da wata sanarwar Allah-wadai da matakin Onafeko.

DSS ta maye zauren majalisar Legas

A wani labarin, mun ruwaito cewa, jami'an hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) dauke da makamai sun mamaye zaure da ginin majalisar dokokin Legas.

Kara karanta wannan

Abba ya zama gwamnan gwamnonin Afrika, an gwangwaje shi a kasar waje

An ce jami'an tsaron sun kuma garkame ofisoshin shugabar majalisar Mojisola Meranda, mataimakinta da sakataren majalisa.

Wata sanarwa daga majalisar Legas, ya nuna cewa, 'yan majalisar sun bayyana matakin da DSS ta dauka a matsayin cin zarafin dimokuradiyya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.