Magana Ta Kare, Kotu Ta Tabbatar da Fitaccen Sarki kan Kujerarsa bayan Rigimar Sarauta

Magana Ta Kare, Kotu Ta Tabbatar da Fitaccen Sarki kan Kujerarsa bayan Rigimar Sarauta

  • Kotun daukaka kara a Ibadan ta yi zama kan rigimar sarauta a jihar Oyo kan kujerar Soun na Ogbomoso
  • Kotun yayin zamanta tabbatar da nadin Oba Ghandi Olaoye a matsayin Soun na Ogbomoso, bayan korafin da aka shigar kan zabensa
  • A baya, kotun Oyo ta soke nadin, tana mai cewa ba a bi ka'idar dokar nadin Soun ba wajen zabensa
  • Alkalin daukaka kara, Mai Shari'a, Nimpar, ya yi watsi da hukuncin kotun farko, wanda ya ba Oba Ghandi damar ci gaba da sarautarsa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Ibadan, Oyo - Kotun daukaka kara da ke zamanta a Ibadan a Oyo, ta yi zama kan rigimar sarautar jihar da aka dade ana yi.

Kotun ta tabbatar da zaben Oba Ghandi Olaoye, Orumogege III, a matsayin Soun na Ogbomoso da ke jihar Oyo.

Kara karanta wannan

'Ba shi da tsoro ko kadan': Abin da Tinubu ya ce bayan babban rashin da Najeriya ta yi

Kotu ta yi hukunci kan tababa da ake man kujerar sarauta
Kotu ta tabbatar da Soun na Ogbomoso a matsayin halastaccen basarake. Hoto: Oba Ghandi Olaoye.
Asali: UGC

Yadda kotu ta tsige Soun na Ogbomoso daga sarauta

Punch ta ruwaito cewa Mai Shari'a, Yargata Nimpar, wanda ya jagoranci kwamitin alkalai uku, shi ya yi hukunci, cewar Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hukuncin ya biyo bayan daukaka karar da Oba Ghandi ya shigar, inda duk kan dalilan 10 na karar suka ci gaba da goyon bayansa.

A baya, Mai Shari'a, K. A. Adedokun na kotun koli ta Oyo ya soke zaben Oba Ghandi a ranar 25 ga Oktoba, 2023, yana mai cewa an yi zaben ne ba bisa ka'ida ba.

Kotu ta tabbatar da nadin Soun na Ogbomoso

Kotun farko ta bayyana cewa ba a bi ka'idodin doka na nadin Soun ba wajen tabbatar masa da sarautar, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Sai dai kotun daukaka kara ta bakin Mai Shari'a, Nimpar ta soke hukuncin kotun farko, wanda ya ba Oba Ghandi damar ci gaba da mulki.

An maka gwamna a kotu kan rigimar sarauta

Kara karanta wannan

"Ba sabani aka ba," Naburaska ya fadi dalilin watsi da Kwankwasiyya

A baya, kun ji cewa rigimar sarauta ta dauki sabon salo bayan dan sarki, Ismaila Owoade ya garzaya kotu, yana son a soke nadin Prince Abimbola Owoade a matsayin Alaafin na Oyo.

Dan Sarkin ya yi korafin ne saboda yana zargin an nada shi ba bisa ka’ida ba inda ya ce bai kamata a nada wani ba tare da Baba Iyaji ya gabatar da sunan wanda ya dace ba.

Kotun ta sanya 11 ga Maris, 2025, don sauraren karar, yayin da Prince Gbadegesin ke kalubalantar matakin Gwamna Seyi Makinde.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.