Tinubu Ya Yi Magana kan Takaddamar Filin BUK, Ya Aika Sako ga Gwamna Abba

Tinubu Ya Yi Magana kan Takaddamar Filin BUK, Ya Aika Sako ga Gwamna Abba

  • Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taɓo batun taƙaddamar da ake yi kan filin jami'ar BUK da unguwannnin da ke makwabtaka da ita
  • Mai girma Bola Tinubu ya buƙaci gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya warware taƙaddamar filin wacce aka ɗauki shekaru ana yi
  • Shugaba Bola Tinubu ya kuma taya ɗaliban jami'ar waɗanda suka kammala digiri na ɗaya da na biyu murnar kammala karatunsu

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kano - Shugaba Bola Tinubu ya yi magana kan taƙaddamar filin da ake yi tsakanin jami'ar BUK da unguwannin da ke makwabtaka da ita.

Shugaba Tinubu ya buƙaci gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya magance taƙaddamar da ake yi kan filin.

Tinubu ya tabo batun takaddamar filin BUK
Tinubu ya bukaci Gwamna Abba ya warware takaddamar filin BUK Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Abba Kabir Yusuf
Asali: Twitter

Tinubu ya yi wannan kira ne a ranar Asabar a Kano yayin bikin yaye ɗalibai karo na 39 a jami’ar BUK, cewar rahoton jaridar The Punch.

Kara karanta wannan

Tinubu: Dan majalisa ya hada Ganduje da El Rufa'i, ya gyara musu zama kan 2027

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ƙaramar ministar ilmi, Farfesa Suwaibu Ahmed, ce ta wakilce shi a wajen taron yaye ɗaliban na jami'ar.

Me Tinubu ya gayawa Gwamna Abba?

Shugaban ya buƙaci gwamnan da ya dauki matakin gaggawa ta hanyar ba da takardar mallakar filin jami’ar domin warware matsalar. Ya jaddada muhimmancin tabbatar da filin jami’ar.

Shugaba Tinubu ya aminta da cewa sabuwar harabar jami’ar ba ta da katanga. Ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya ta ware kuɗi don gudanar da aikin.

“Gwamnatin tarayya ta riga ta samar da kuɗaɗen, kuma za a fara aikin."

- Shugaba Bola Tinubu

Ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na inganta gine-ginen jami’o’i a faɗin ƙasar nan.

Shugaban ƙasan ya taya murna ga ɗalibai 3,400 na jami'ar da suka kammala karatun digiri na biyu.

Hakazalika ya yabawa ɗalibai 8,769 da suka kammala digirinsu na farko a makon da ya gabata.

Tinubu ya samu yabo

Shugaban jami’ar, Farfesa Sagir Abbas, ya jinjinawa Tinubu bisa kafa hukumar NELFund, wacce ke ba da rancen kuɗi ba tare da ruwa ba ga dalibai masu ƙaramin ƙarfi, don tallafa musu.

Kara karanta wannan

'Dan majalisa ya fadi dalilin kara N700bn a kasafin kudin 2025

Hakazalika, Sagir Abbas ya yabawa Tinubu bisa cire jami’o’in tarayya daga tsarin IPPIS, wanda hakan ya dawo da ikon jami’o’in wajen daukar ma’aikata da biyan albashinsu.

Tinubu ya yi wa manyan Arewa laifi

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon hadimin Shugaba Muhammadu Buhari, ya yi magana kan laifin da wasu manyan ƴan Arewa suke jin Bola Tinubu ya yi musu.

Ismaeel Ahmed ya bayyana cewa wasu manyan Arewa na jin cewa Shugaba Tinubu ya ajiye su a gefe, duk kuwa da irin ƙoƙarin da suka yi masa a zaɓen 2023.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng