'Akwai Jahilci': Tsohon Ministan Sadarwa a Mulkin Buhari Ya Caccaki Masu Sukar Shari'a

'Akwai Jahilci': Tsohon Ministan Sadarwa a Mulkin Buhari Ya Caccaki Masu Sukar Shari'a

  • Tsohon ministan sadarwa, Adebayo Shittu, ya soki masu adawa da kafa kwamitin shari'ar Musulunci a Kudu maso Yamma, yana cewa jahilci ne ke haddasa hakan
  • A cewarsa, kwamitocin sun dade suna gudanar da shari’o’in addini a wasu jihohi ba tare da haddasa wata matsala ba
  • Ya kara da cewa Musulmi suna da ’yancin gudanar da harkokinsu bisa doka ta shari'a, don haka gwamnati ba ta da ikon hana su yin hakan

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Ibadan, Oyo - Tsohon ministan sadarwa, Adebayo Shittu, ya soki masu adawa da kwamitin shari'ar Musulunci a Kudu maso Yamma.

Mr. Shittu ya ce adawar da ake yi jahilci ne saboda kwamitocin sun dade suna gudanar da shari’o’i na addini a wasu jihohi ba tare da wata matsala ba.

Kara karanta wannan

Lauyoyi da ma'aikata sun hango mutuwa ana cikin shari'a, sun yi rige rigen ficewa daga kotu

Ministan Buhari ya caccaki masu sukar shari'ar Musulunci
Tsohon minista a mulkin Buhari ya magantu kan dambarwar da ake yi game kafa kotunan Shari'ar Musulunci. Hoto: Adebayo Shittu.
Asali: Twitter

Tsohon minista ya magantu kan kafa Shari'a

Daily Trust ta ruwaito cewa kungiyoyi da shugabannin gargajiya sun nuna rashin goyon baya, amma Shittu ya ce rashin sani ne ke haddasa hakan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewarsa, kwamitocinsu sun dauki lokaci mai tsawo suna suna gudanar da shari’o’i inda ya hakan ’yanci ne na Musulmi.

"Ina ga bambanci idan Musulmi sun yi aure a masallaci bisa doka ta shari'a, amma idan suna son saki, sai a kai su kotun gargajiya?"
"Abin da hankali ya kamata ya fahimta shi ne, dokar da aka yi aure a cikinta ita ce ya kamata a yi amfani da ita wajen saki.
"Shin, an taba tursasa wani Kirista ko wanda ba musulmi ba zuwa kotun shari'a?"

- Adebayo Shittu

Shari'a: Tsohon minista ya musanta zargin haddasa rudani

Shittu ya musanta zargin cewa kafa kwamitocin zai haddasa rudani, yana mai cewa suna aiki a Oyo da Legas tun fiye da shekara goma.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun fara taɓa manya, an yi garkuwa da shugaban hukumar zaɓe ta jiha

Ya ce Musulmi suna da ’yancin tafiyar da al’amuransu bisa tsarin addininsu, don haka ba daidai ba ne a hana su yin hakan.

"Ina fata Musulmi a jihohin nan za su kai gwamnati da masu kawo musu cikas kotu."

- Adebayo Shittu

Basarake ya soki tsarin shari'ar Musulunci

Kun ji cewa Basarake Oba Omo Tooyosi Akinleye ya bayyana rashin dacewar kafa shari'ar Musulunci a Kudu maso Yamma, ya ce hakan zai haddasa rikici.

Basaraken ya jaddada cewa tsarin dimokuradiyya ya fi dacewa, domin yana bai wa kowa 'yancin addini ba tare da fifita wata akida ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

iiq_pixel