Jarrabawa Ta Sake Faɗawa Mutane, Tanka Maƙare da Fetur Ta Kama da Wuta a Kusa da Gidaje

Jarrabawa Ta Sake Faɗawa Mutane, Tanka Maƙare da Fetur Ta Kama da Wuta a Kusa da Gidaje

  • Wata tanka maƙare da man fetur ta yi bindiga tare da kamawa da wuta a Ibadan, ta kashe direba tare da jikkata yaron motar
  • An ruwaito cewa tankar ta ci karo da wasu manyan motoci bayan ta kufce wa direban, sannan ta faɗa wani rami da ke kusa da babban titin Ojoo zuwa Iwo
  • Hukumar kashe gobara ta jihar Oyo ta bayyana cewa jami'anta sun yi nasarar kashe wutar da ta kama bayan faɗuwar tankar

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ibadan, jihar Oyo - Wata tanka dauke da man fetur ta yi bindiga a tsakiyar gidajen mutane, ta kashe direbanta tare da jikkata wani mutum guda a Ibadan.

Babban manajan hukumar kashe gobara ta jihar Oyo, Mista Yemi Akinyinka, ya tabbatar da lamarin a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai ranar Laraba a Oyo.

Kara karanta wannan

Sojoji su na ragargaza, an kai samamen dare a maboyar Boko haram

Taswirar Oyo.
Mutum 1 ya mutu da wata tankar fetur ta fashe a Ibadan, babban birnin Oyo Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Tankar mai ta kama da wuta a Ibadan

Ya bayyana cewa tankar ta kucce wa direban, ta yi karo da wasu manyan motoci guda biyu, sannan ta kife a wani rami da ke kusa da titin ta kama da wuta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mista Akinyinka ya ce hatsarin ya yi sanadiyyar mutuwar direban tankar yayin da aka ceto yaron motar da ransa duk da ya jikkata, Vanguard ta tattaro.

“Wannan mummunan lamarin mara daɗi ya faru ne a kusa da gidan Fijabi da ke Agbowo, kan babban titin Ojoo zuwa Iwo a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.
“Mun samu kiran gaggawa kan gobarar da ta kama bayan faɗuwar tankar da misalin ƙarfe 2:45 na safe ta wayar tarho.
“Mun hanzarta tura ma’aikata zuwa wurin, inda suka dakile yaduwar gobarar zuwa gidajen mutane da ke kusa.”

- Yemi Akinyinka.

Faɗuwar tankar ya shafi wasu motoci 3

Shugaban hukumar kwana-kwana ta Oyo ya ƙara da cewa da zuwan jami'an kashe gobara, sun tarar da motoci sun kama da wuta a wurin, rahoton Tribune.

Kara karanta wannan

Wata tankar man fetur ta sake fashewa a jihar Neja, ana fargabar mutane sun mutu

“Da muka isa wurin, mun tarar da manyan motoci uku suna ci da wuta, kowace mota tana da nisan mitoci 20 tsakaninta da wata."
“Direban tankar ya kone kurmus yayin da muka yi nasarar ceto yaron motar a raye, kuma yanzu haka an kai shi Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ibadan (UCH) domin kula da lafiyarsa," in ji shi.

Ibadan: Tankar ta ƙone a hatsarin

Akinyinka ya bayyana cewa tankar ta lalace gaba ɗaya sakamakon gobarar, amma an samu damar ceto sauran manyan motocin guda biyu daga lalacewa.

Ya ce shugaban sashen ayyuka na hukumar kashe gobara Mista Ismail Adeleke, tare da tawagarsa, ‘yan sanda, da sauran jami’an tsaro, sun kasance a wurin domin tabbatar da tsaro da hana tashin hankalin jama’a.

Gobara ta babbake kayan miliyoyi a Ibadan

A wani labarin, kun ji cewa ƴan kasuwa sun tafka asara da wata mummunar gobara ta tashi da tsaɗkar dare a kasuwar sayar da kayan gyara a Ibadan.

Kara karanta wannan

An shiga jimami bayan tankar mai ta sake fashewa a Najeriya, mutane 11 sun rasu

Gobarar wanda ta fara ci da karfe 2:00 na tsakar dare ta yaɗu zuwa shagunan ƴan kasuwa duk da ƙoƙarin jami'an kwana-kwana na kashe ta.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262