'Muna kan Tsari': Abba Kabir Ya Magantu bayan Hukuncin Kotu, Ta ba Yan Kano Shawara

'Muna kan Tsari': Abba Kabir Ya Magantu bayan Hukuncin Kotu, Ta ba Yan Kano Shawara

  • Gwamnatin jihar Kano ta yi magana bayan Kotun Daukaka Kara ta yi hukunci kan rigimar masarauta da ake yi
  • Gwamnatin ta yaba wa hukuncin Kotun Daukaka Kara da ya tabbatar da sahihancin matakan da aka dauka kan al’amuran masarautun jihar
  • Kotun ta warware hukuncin da Kotun Tarayya ta yi a baya, tana mai tabbatar da dokokin da suka shafi nadin sarakuna da gyaran masarautun jihar
  • Kwamishinan shari'a, Haruna Dederi ya bayyana cewa hukuncin ya tabbatar da adalci da bin ka’ida, tare da tabbatar da ci gaba da kare al’adun gargajiya na jihar Kano

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Kano - Gwamnatin Kano ta mayar da martani da Kotun Daukaka Kara ta yi hukunci kan rigimar masarauta a jihar.

Gwamnatin ta yaba wa hukuncin da Kotun Daukaka Kara, reshen Abuja, ta yanke kan batun masarautu da ya shafi tsohon Sarkin Kano na 15, Muhammadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero.

Kara karanta wannan

Sarauta: Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yi Hukunci a Rikicin Aminu da Sanusi II

Gwamnatin Kano ta magantu kan hukuncin kotu game da masarautu
Gwamnatin Kano ta yaba wa kotu bayan hukunci game da rigimar sarauta. Hoto: Abba Kabir Yusuf, Masarautar Kano.
Source: Twitter

Gwamnatin Kano ta magantu bayan hukuncin kotu

Antoni-janar na jiha kuma Kwamishinan Shari’a, Haruna Dederi shi ya bayyana hakan a ranar Asabar 11 ga watan Janairun 2025, cewar Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewarsa, hukuncin kotun ya warware matakan Kotun Tarayya ya tabbatar da cewa matakan gwamnati kan nadin sarakuna da gyaran masarautu na bisa doka.

Ya ce hakan ya tabbatar sahihancin matakan gwamnatin Kano da kuma kara musu karfin guiwa kan lamarin masarautun.

"Hukuncin Kotun Daukaka Kara ya tabbatar da sahihancin matakan gwamnati, ya kuma karfafa mana gwiwar ci gaba da kawo gyara ga tsarin gargajiya."
“Dukkan hukunci da umarni da Kotun Tarayya Kano ta bayar an soke su gaba daya ta hanyar hukuncin Kotun Daukaka Kara.”

- Haruna Dederi

Umarnin gwamnatin Kano bayan hukuncin kotu

Dederi ya kara da cewa hukuncin ya fayyace inda hurumin shari’a yake a kan batun nadin sarauta, yana tabbatar da dokokin kundin tsarin mulki.

Kara karanta wannan

Magana ta dawo sabuwa, kotu ta ba Ministocin Tinubu 2 umarni kan kudirin haraji

Ya ce hukuncin ya nuna cewa gwamnatin jihar na aiki da ka’ida da adalci wajen yin gyare-gyare a masarautun gargajiya tare da kare al’adun jihar Kano.

Har ila yau, ya ce dokar da Majalisar Dokokin jihar Kano ta yi dangane da masarautu, da duk matakan da gwamna ya dauka, an tabbatar da su.

Saboda haka, dukkan hukumomi na gwamnati da na masu zaman kansu da jama’a an wajabta musu bin hukuncin Kotun Daukaka Kara ba tare da bata lokaci ba.

Gwamnatin jihar ta jaddada kudirinta na tabbatar da bin doka da adalci don ci gaba da inganta tsarin gargajiya, tare da tabbatar da wakilci da cigaban al’umma.

Kano: Kotu ta yi hukunci kan rigimar sarauta

Kun ji cewa Kotun Ɗaukaka Ƙara ta soke umarnin da Babbar Kotun Jihar Kano ta bayar, wanda ya hana wasu sarakunan gargajiya na jihar kiran kansu a matsayin sarakuna.

Wani kwamitin alkalai uku, karkashin jagorancin Mai Shari’a Mohammed Mustapha, ya bayyana cewa hukuncin Kotun Kano na ranar 15 ga Yuli, 2024 ya ci karo da ka’idojin adalci ga kowane bangare.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.