'Ka Kawo Cigaba a Najeriya': Jonathan Ya Tura Sakon Yabo da Buhari Ya Cika 82

'Ka Kawo Cigaba a Najeriya': Jonathan Ya Tura Sakon Yabo da Buhari Ya Cika 82

  • A yau Talata 17 ga watan Disambar 2024, tsohon shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari ya cika shekaru 82 a duniya
  • Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya taya Buhari murnar wannan rana ta zagayowar ranar haihuwarsa
  • Jonathan ya yi masa fatan samun karin lafiya da kwanciyar hankali inda ya yaba masa kan cigaban da ya kawo kasa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Tsohon Shugaban Kasa, Goodluck Jonathan ya taya Muhammadu Buhari murnar zagayowar ranar haihuwarsa.

Goodluck Jonathan ya taya Muhammadu Buhari murna ne bayan ya cika shekaru 82 tare da yi masa fatan alheri da lafiya da kwanciyar hankali.

Jonathan ya taya Buhari murnar zagayowar ranar haihuwarsa
Goodluck Jonathan ya yabawa salon mulkin Muhammadu Buhari. Hoto: Muhammadu Buhari.
Asali: Facebook

Jonathan ya yaba salon mulkin Buhari

Jonathan ya bayyana hakan a cikin wata sakon taya murna da ya sanyawa hannu a yau Talata 17 ga watan Disambar 2024, cewar Tribune.

Kara karanta wannan

Ana shirin ballowa tsohon gwamna ruwa, ya yi barazana ga masu son hada shi da Tinubu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tsohon shugaban kasar ya yabawa Muhammadu Buhari kan rawar da ya taka wajen tabbatar da hadin kai da cigaban kasa.

“A madadin ni kai na da iyalaina, ina mika sakon taya murna gare ka a wannan rana ta musamman.'"
"A wannan rana ta haihuwa, ina addu’a Allah ya ba ka lafiya, hikima da farin ciki.
“Ina kuma amfani da wannan dama don jaddada yabo ga jajircewarka wajen cigaban kasa da bunkasarta."

- Goodluck Jonathan

Jonathan ya yi wa Buhari fatan alheri

Yayin da yake masa fatan farin ciki a wannan rana ta musamman, Jonathan ya yi masa fatan kusanci da masoyansa, The Nation ta ruwaito.

“Ina fatan wannan sabuwar shekara a rayuwarka za ta kara kusanci tsakaninka da masoyanka."
"Ina kuma fatan ranar haihuwarka ta kasance cike da kauna da farin ciki, ka karbi sakon taya murna ta musamman a wannan ranar haihuwarka.”

- Goodluck Jonathan

Kara karanta wannan

2027: Jam'iyyar APC ta yi zazzafan martani kan ziyarar Kwankwaso ga Obasanjo

Basarake ya yabawa mulkin Buhari

Kun ji cewa fitaccen basarake a Kudancin Najeriya ya kai ziyara ga tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari a jihar Katsina.

Ooni na Ife, Oba Adeyeye Ogunwusi ya yabawa tsohon shugaban kasar lokacin da yake mulkin Najeriya da cewa ya taka rawa .

Basaraken ya ce abin mamaki Buhari ya kara murmurewa kaman wani matashi duk da shekarun da yake da shi a duniya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

iiq_pixel