'Yan Bindiga Sun Kai Harin Ban Mamaki, Sun Kashe Wata Yar Kasuwa da Malamin Addini
- Ƴan bindiga sun kutsa har cikin gida, sun kashe wata ƴar kasuwa da limamin coci a Jalingo, babban birnin jihar Taraba
- Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar ƴan sandan jihar, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce akwai abin mamaki a hare-haren
- Abdullahi Usman ya ce maharan sun shiga gidajen mutanen biyu, suka kashe su su ba tare da ɗaukar ko da allura ba
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Taraba - Wasu ‘yan bindiga sun kashe wata ‘yar kasuwa a unguwar Mayo Dasa da ke cikin Jalingo, babban birnin jihar Taraba.
Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne da tsakar daren Juma’a 6 ga Disamba, 2024.

Source: Facebook
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Taraba, Abdullahi Usman ya tabbatar da hakan ga Channels tv ta wayar tarho.
'Miyagun 'yan bindiga sun kashe 'yar kasuwa
Jami'in ya ce a lokacin da ‘yan bindigar suka kutsa kai cikin gidan matar, sun yi amfani da adduna wajen karya tagar gidan.
Abdullahi Usman ya ce a bayanin da suka samu, maharan sun bindige matar tana tsakiyar karatun jarabawa, harsashin ya fasa ta bayanta ya ɓullo cikinta.
Kakakin ƴan sandan ya ce:
"Tana cikin karatu a ɗakinta a shirye-shiryen jarabawar da suka fara, ba zato ba tsammani maharan suka kutsa kai suka buɗe mata wuta.
"Sun harbe ta a baya harsashi ya shiga ya fito ta cikinta. Lokacin da suka fasa tagogin mutanen da ke zaune a gidan sun fito a tsorace amma abin mamakin ba su tafi da kowa ba.
Mai magana da yawun ƴan sandan ya kuma ƙara da cewa bincikensu ya nuna maharan ba su ɗauki komai ba a gidan, kashe matar kawai suka yi.
Ƴan bindiga sun hallaka malamin coci
Hari na biyu da aka kai a cewar kakakin ‘yan sandan ya faru ne a unguwar Jerbanbur da ke Jalingo.
Abdullahi Usman ya ce wasu ƴan bindigar sun buɗewa limamin coci wuta har ya mutu kuma ba su ɗauki ko da allura ba a gidan.
Ya ce waɗannan hare-haren abin mamaki ne da al'ajabi domin ƴan bindigar sun saba kisa, su sace mutane don neman kuɗin fansa, rahoton Daily Post.
Taraba: Maharan sun kashe manomi
A wani labarin, kun ji cewa ƴan bindiga sun kashe wani fitaccen manomi, sun sace wasu da dama a jihar Taraba da ke Arewa maso Gabas.
Majiyoyi daga yankin sun bayyana cewa ƴan bindiga sun buƙaci a ba su maƙudan kuɗin fansa kafin su saki manoman da suka sace.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng

