Majalisa Ta Yi Adawa da Yi wa Dokar Shari'ar Muslunci Kwaskwarima a Tsarin Mulki

Majalisa Ta Yi Adawa da Yi wa Dokar Shari'ar Muslunci Kwaskwarima a Tsarin Mulki

  • Majalisar wakilai ta ki amincewa da yi wa sassan da su ka yi magana kan shari'ar Musulunci a kundin tsarin mulki gyara
  • Dan Majalisa Aliyu Misau ya bukaci majalisa ta amince a cire kalmar da ke danganta shari'ar ga mutane kawai
  • Ya ce kamfanonin Musulunci irinsu bankunan JAIZ da Taj ba za su samu damar Shari'a da su ke bukata ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT Abuja - Majalisar wakilan Najeriya ta yi fatali da ƙudurin da ya nemi a yi wa wasu sassa na kundin tsarin mulkin ƙasa na 1999 kwaskwarima.

Ɗan majalisar PDP, Aliyu Missau ya gabatar da ƙudirin da ke neman a cire wata kalma da ta gabaci shari'ar Muslunci a kundin tsarin mulkin amma takwarorinsa na ganin zai saba tsarin Najeriya.

Kara karanta wannan

Yadda ake muzgunawa Musulmi a Turai duk da ikirarin sanin hakkin dan adam

Majalisa
Majalisa ta ki amincewa da gyara sashen Shari'ar Muslunci a kundin tsarin mulki Hoto: House of Representatives
Asali: Facebook

Jaridar The Cable ta tattara cewa dan majalisar na son a yi gyara ga sashe na 24, 262, 277 da 288 na kundin tsarin mulki.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sashen da ɗan Majalisa ya so a gyara

Jaridar Daily Post ta tattara cewa dan Majalisa ya nemi a cire kalmar 'ƙashin kai' daga sashen da ya jiɓanci shari'ar Musulunci a kundin tsarin mulkin ƙasa

Aliyu Misau ya ce kalmar 'ƙashin kai' da a turance ga zo a 'personal' a dokar ta tauye kamfanonin da ke bin tsarin musulunci irinsu bankin JAIZ da Taj.

Abin da sashen shari'ar Musulunci ya ƙunsa

Sashen da Aliyu Misau ke son a gyara zai tabbatar da kalmar Shari'ar Muslunci ta tsaya da kafarta ba tare da jingina ta da daidaikun mutane ba.

Abin da sashen ya ƙunsha;

"Kotun daukaka kara ta Shari'a, baya ga sauran hukunce-hukuncen da wata doka ta Majalisar Dokoki ta kasa za ta ba ta, za ta yi amfani da irin wannan hukunci da ikon sa ido a cikin shari'o'in da su ka shafi jama'a kan shari'ar Musulunci."

Kara karanta wannan

'Yadda 'yan ta'adda ke samun bindigogi da harsasan gwamnati,' sojoji sun yi bayani

Majalisa na son a daure iyayen yara

A baya kun kun ji cewa majalisar dattawan Najeriya ta fara tunanin bijiro da wani ƙuduri da zai ba kotuna damar hukunta iyayen yara marasa zuwa makarantu a fadin ƙasar.

Wannan ya biyo bayan karuwar yara marasa zuwa makaranta da shugaban majalisar Godswill Obot wuya ce yawansu ya kai aƙalla yara miliyan 20.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.