Sarakuna Sun Haɗa Baki, Sun Kai Karar Basarake gaban Gwamna, Sun Roki Alfarma

Sarakuna Sun Haɗa Baki, Sun Kai Karar Basarake gaban Gwamna, Sun Roki Alfarma

  • Wani basarake ya shiga matsala bayan zarginsa da neman handame wasu filaye a jihar Osun da ke Kudancin Najeriya
  • Ogiyan na Ejigbo, Oba Omowonuola Oyeyode ya kai karar Olusongbe na Songbe, Oba Kamilu Ojelabi gaban gwamnan jihar
  • Wannan na zuwa ne yayin da gamayyar sarakuna 19 suka bukaci gwamnan ya yi bincike kan matsalar filaye da ake zargin basarake

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Osun - Gamayyar sarakunan gargajiya sun kai korafin dan uwansu wurin Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun.

Sarakunan sun kai karar basarake, Olusongbe na Songbe, Oba Kamilu Ojelabi kan zargin neman cinye wasu filaye.

Sarakunan gargajiya sun yi korafi gaban gwamna kan wani basarake
Wasu sarakunan gargajiya a jihar Osun sun kai karar wani basarake ga Gwamna Ademola Adeleke. Hoto: Ademola Adeleke.
Asali: Facebook

Sarakuna na zargin basarake da kwace filaye

Kara karanta wannan

Bayan shafe shekaru a kasan Kwankwaso, Ganduje ya fadi illar zama mataimakin gwamna

Punch ta ce Ogiyan na Ejigbo, Oba Omowonuola Oyeyode a madadin sauran sarakunan shi ya kai korafin gaba gwamna.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Oba Oyeyode ya bukaci gwamnan da ya kira basaraken da ake zargi domin yi masa tambayoyi kan lamarin.

Ya kuma roki Gwamna Adeleke ya gabatar da binciken a bainar jama'a domin ya zama izina ga wasu da ke shirin yin haka.

"Ya kamata gwamnan ya kira Ojelabi domin yi masa tambayoyi kan abin da ake zarginsa, kuma bayan bincike a wallafa saboda kowa ya gani."

- Oba Omowonuola Oyeyode

Musabbabin zargin basaraken a Osun da ake yi

A cikin sanarwar da sarakunan suka sanyawa hannu, sun zargi basaraken da shiga gonar da ba ta shi ba kan mallakar wasu yankuna a karamar hukumar Ejigbo da ke jihar.

Sarakunan suka ce Olusongbe ya ayyana kansa mamallakin yankuna da dama da suka hada da Idigba da Olorin da Ibogunde da Imoru da Omolosan da kuma Bada da sauran wurare.

Kara karanta wannan

An zo wurin: Kotu ta yi zama kan zargin Ganduje da almundahana, ta shirya yanke hukunci

Yadda aka fatattaki basaraken a fada

Kun ji cewa Mai Martaba Ooni na Ife, Oba Adeyeye Enitan Ogunwusi ya fadi wasu abubuwan da suka faru tsakanin shi da wani sarki.

Oba Adeyeye Enitan Ogunwusi ya ce wata rana ya ziyarci fadar Oluwo na Iwo Oba Abdulrasheed Akanbi amma abin bai yi kyau ba.

An ruwaito cewa Oba na Iwo, Abdulrasheed Akanbi ya saba da gardagi ga masu bautar gumaka a Osun da ma kasar Yarabawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.