Gwamna Abba Kabir Ya Nada Ahmed Musa Mukami a Gwamnatinsa

Gwamna Abba Kabir Ya Nada Ahmed Musa Mukami a Gwamnatinsa

  • Gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta ba kyaftin ɗin tawagar ƴan wasan Super Eaglee, Ahmed Musa muƙami
  • Gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa Ahmed Musa a muƙamin jakadan wasanni na jihar Kano
  • Ɗan wasan na ƙungiyar Kano Pillars ya miƙa saƙon godiyarsa ga gwamnatin bisa wannan naɗin da ta yi masa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kano - Gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta ba Ahmed Musa muƙami.

Gwamna Abba Kabir ya naɗa kyaftin ɗin na Super Eagles a matsayin jakadan wasanni na jihar Kano.

Gwamna Abba ya nada Ahmed Musa mukami
Gwamna Abba Kabir ya ba Ahmed Musa mukami Hoto: @Ahmedmusa718, @KyusufAbba
Asali: Twitter

Ahmed Musa ya sanya takardar naɗin a shafinsa na X mai ɗauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar Kano, Abdullahi Baffa Bichi a ranar Laraba, 23 ga watan Oktoban 2024.

Kara karanta wannan

Tinubu na korar ministoci, gwamna ya amince zai biya albashin N80,000

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cikin sanarwar, sakataren gwamnatin na Kano ya tabbatar da cewa naɗin zai fara aiki ne daga ranar, 24 ga watan Yulin 2024.

"Ina matuƙar farin farin ciki sanar da kai cewa mai girma Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya amince da naɗin ka a matsayin jakadan wasanni na jihar Kano daga ranar 24 ga watan Yuli, 2024."

- Abdullahi Baffa Bichi

Ahmed Musa ya yi godiya

Kyaftin ɗin na Super Eagles ya miƙa saƙon godiyarsa kan wannan naɗin da gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi masa.

"Ina matuƙar farin ciki da aka naɗa ni jakadan wasanni na jihar Kano!"

"Ina godiya ga gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa wannan gagarumin nauyi da dama. A tare za mu zaburar da matasa masu tasowa don cimma nasarori a ciki da wajen fili. Mu zo mu kafa tarihi!"

Kara karanta wannan

Mafi karancin albashi: Gwamnan jihar Arewa ya amince zai biya N75,000

- Ahmed Musa

An naɗa Ahmed Musa sarauta

A wani labarin kuma, kun ji cewa shahararren ɗan wasan Najeriya, Ahmed Musa ya samu sarautar gargajiya ta 'Shetiman Kwallon Kafar Nguru' a yau Lahadi, 9 ga watan Yunin 2024.

Sarkin Nguru, Alhaji Mustapha Ibn Mai Kyari ne ya naɗa keftin din tawagar Super Eagles wannan saurata bayan wata ziyara da ya kai fadarsa da ke Nguru, jihar Yobe.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng