Tinubu Na Korar Ministoci, Gwamna Ya Amince Zai Biya Albashin N80,000

Tinubu Na Korar Ministoci, Gwamna Ya Amince Zai Biya Albashin N80,000

  • Gwamnatin Akwa Ibom ta sanar da mafi ƙarancin albashin da za ta biya ma'aikatan jihar da ke yankin Kudu maso Kudu
  • Gwamnatin ƙarƙashin jagorancin Umo Eno ta sanar da cewa za ta biya ma'aikatan jihar sabon mafi ƙarancin albashi na N80,000 a wata
  • Kwamishinan labaran jihar ya sanar da hakan inda ya ƙara da cewa an kafa kwamitin da zai tabbatar da an aiwatar da ƙarin albashin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Akwa Ibom - Gwamnatin jihar Akwa Ibom ta sanar da biyan mafi ƙarancin albashi na N80,000 ga ma’aikatanta. 

Kwamishinan yaɗa labaran jihar, Mista Ini Ememobong, ya bayyana cewa biyan N80,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ya nuna cewa gwamnatin ta himmatu wajen kyautata jin daɗin ma’aikata.

Kara karanta wannan

Mafi karancin albashi: Gwamnan jihar Arewa ya amince zai biya N75,000

Gwamnan Akwa Ibom zai biya albashin N80,000
Gwamna Umo Eno ya amince da biyan ma'aikata albashin N80,000 Hoto: Pastor Umo Eno
Asali: Twitter

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Ini Enemobong ya sanyawa hannu ranar Laraba a Uyo, babban birnin jihar Akwa Ibom, cewar rahoton jaridar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Uno zai biya albashin N80,000

Ememobong ya bayyana cewa Gwamna Umo Eno ya kafa kwamitin da zai tabbatar da aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashin, rahoton jaridar Vanguard ya tabbatar.

"Gwamnan Akwa Ibom, Fasto Umo Eno, ya bayyana cewa gwamnatin jihar za ta biya sabon mafi ƙarancin albashi na N80,000 ga ɗaukacin ma’aikatan jihar."
"Domin tabbatar da gudanar da wannan tsarin, gwamnan ya kuma kafa kwamitin aiwatarwa, wanda aka ba shi wata ɗaya ya gabatar da rahotonsa kan yadda za a yi ƙarin albashin."

- Ini Ememobong

Kwamitin mai mambobi 15 da shugaban ma’aikatan gwamnati, Elder Effiong Essien ke jagoranta ya ƙunshi shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago na NLC da TUC.

Kara karanta wannan

Sankara: Kotu ta ba 'yan sanda umarni kan kwamishinan Jigawa da aka dakatar

Akwai 'yan ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta Najeriya (NULGE) da sauransu.

Karanta wasu labaran kan mafi ƙarancin albashi

Gwamna zai biya albashin N75,000

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya amince da biyan sabon mafi ƙarancin albashi ga ma'aikata.

Gwamna Nasir Idris ya amince da N75,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan gwamnatin jihar da ke yankin Arewa maso Yamma.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng