A Karshe, Tinubu Ya Ji Korafe Korafen Yan Najeriya, Ya Sallami Ministoci 5
- Shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya ji kiraye-kirayen al'umma da ya sallami wasu Ministoci guda biyar
- Shugaban ya dauki matakin ne a yau Laraba 23 ga watan Oktoban 2024 yayin zaman Majalisar zartarwa da aka yi
- Daga cikin Ministocin da aka kora akwai ta harkokin mata da karamin Ministan gidaje da raya birane, Abdullahi Gwarzo
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
FCT, Abuja - Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya sallami wasu Ministoci guda biyar a gwamnatinsa.
Bola Tinubu ya dauki wannan mataki ne bayan kiraye-kiraye da yan kasar ke yi masa na ya sallami wasu daga ministoci.

Source: Facebook
Jerin Ministoci da Bola Tinubu ya sallama
Channels TV ta tabbatar da cewa Bola Tinubu ya sallami Ministocin ne a yau Laraba 23 ga watan Oktoban 2024.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Daga cikin wadanda abin shafa akwai Ministar harkokin mata, Uju-Ken Ohanenye da Ministan yawon buɗe ido, Lola Ade-John, cewar Punch.
Sauran sun hada Ministan ilimi, Tahir Mamman da Abdullahi Gwarzo wanda ke riƙe da mukamin karamin Ministan gidaje da raya birane da kuma Ministar matasa, Jamila Ibrahim.
Sauyi a ma'aikatar wasanni
Har ila yau, bayan rusa ma'aikatar harkokin wasanni, Tinubu ya nada Shehu Dikko a matsayin shugaban hukumar wasanni (NSC).
Dikko shi zai jagoranci maiakatar bayan sallamar Ministanta, Sanata John Enoh domin kawo sauyi a harkokin wasanni.
Karanta wasu labaran kan Ministoci a Najeriya
Ana Dakon Korar Ministoci, Tinubu Ya Rushe Ma'aikatu, Ya Yi Garambawul a Gwamnati
Ministoci Sun Firgita da Dawowar Tinubu, An Fadi Lokacin da Ake Ganin Zai Kori Wasu
Shugaba Tinubu Ya Aika Muhimmin Saƙo Ga Ministoci 5 da Ya Kora Daga Aiki

Kara karanta wannan
Ana dakon korar Ministoci, Tinubu ya rushe ma'aikatu, ya yi garambawul a gwamnati
Tinubu ya nada sababbin Ministoci a gwamnatinsa
Kun ji cewa jim kadan bayan sallamar wasu Ministoci da sauye-sauye a gwamnatinsa, Bola Tinubu ya nada sababbi.
Tinubu ya amince da nadin Bianca Odinaka Odumegu-Ojukuwu a matsayin ƙaramar Ministar harkokin waje.
Sauran sun hada Dakta Nentawe Yilwatda a matsayin Ministan jin kai da walwala da Muhammadu Maigari Dingyadi a ma'aikatar ayyuka da kwadago.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng
