Gwamna Ya yi Barazanar Sauke Sarakuna saboda Rashin Tsaro

Gwamna Ya yi Barazanar Sauke Sarakuna saboda Rashin Tsaro

  • Gwamnatin jihar Taraba ta gargadi sarakunan gargajiya kan tashin hankali da ake yawan samu a yankunan da suke mulki
  • Mataimakin gwamnan jihar, Aminu Muhammad Alkali ne ya wakilci gwamna Agbu Kefas yayin wani taron samar da zaman lafiya a Taraba
  • Sarakunan gargajiya a jihar Taraba sun nuna amincewa da cigaba da samar da zaman lafiya da ɗaukar matakan da za su kawo cigaba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Taraba - Gwamantin jihar Taraba ta yi kira na musamman ga sarakunan gargajiya kan muhimmacin samar da zaman lafiya.

Gwamna Agbu Kefas wanda ya samu wakilci ya ce gwamnati za ta dauki mataki mai tsauri a kan duk wani sarki da aka samu da hannu kan rashin tsaro.

Kara karanta wannan

Ana rade radin rigimar Abba da Kwankwaso, an kori yan jaridu daga gidan gwamnati

Kefas
Gwamnatin Taraba ta gargadi sarakuna. Hoto: Taraba State Government
Asali: Twitter

Jaridar Daily Trust ta wallafa cewa gwamnatin Taraba ta yi gargaɗin ne yayin wani taron zaman lafiya a karamar hukumar Karim Lamido.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna ya yi barazana ga sarakuna

Gwamnan Taraba, Agbu Kefas ya yi barazanar sauke duk wani sarki da aka samu da hannu kan matsalar tsaro.

Mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdullahi Alkali ya ce daga yanzu gwamnati ba za ta lamunci tayar da rikici ba a kowane yanki.

An yi rikici tsakanin Fulani da Gommu

An samu rikici tsakanin yan ƙabilar Fulani da Gommu a karamar hukumar Karim Lamido inda aka rasa rayuka.

Gwamna Agbu Kefas ya ce ranshi ya ɓaci matuka kan lamarin kuma sanadiyyar haka ne ma ya dauki matakin tura mataimakinsa garin.

Sarakuna sun yi magana a Taraba

Sarkin kauyen Bikwin, Bitrus Bala Sarkin Yara ya bayyana cewa za su cigaba da ƙoƙarin samar da zaman lafiya a jihar Taraba.

Kara karanta wannan

Gwamna a Arewa ya hango haɗari, ya rufe manyan makarantun kuɗi nan take

Shugaban kungiyar Tabbital Fulani, Ardo Njarenga Galdo ya ce dole a rika jan hankulan matasa idan ana son samun zaman lafiya a jihar.

An kama masu taimakon yan bindiga

A wani rahoton, kun ji cewa an kama mata da miji cikin wadanda ake zargi da adana makamai da yan bindiga a jihar Taraba.

Rahotanni sun nuna cewa an kama mata da mijin ne a karamar hukumar Lau ta jihar tare da wani mutum da suke aiki tare.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng