NDLEA: Sanata Ya Yi Kakkausan Martani kan Zargin Kama Kwayoyi a Gidansa

NDLEA: Sanata Ya Yi Kakkausan Martani kan Zargin Kama Kwayoyi a Gidansa

  • Sanatan da ke rigima da NDLEA, Oyelola Ashiru ya karyata zargin da hukumar ke yi masa na ta'ammali da miyagun kwayoyi
  • A sanarwar da hadimin Sanatan, Olaitan Adeyanju ya fitar a ranar Litinin, ya bayyana cewa NDLEA na yi masa kazafi ne kawai
  • Shugaban hukumar NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa mai ritaya ne ya ce an kama kwayoyi a gidan Sanatan da ke Kwara

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Sanata mai wakiltar Kwara ta Kudu, Oyelola Yisa Ashiru ya zargi hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) da yi masa kazafi.

Kara karanta wannan

Jami'ai sun kama kwayoyi a gidan Sanatan da yake so a rusa hukumar NDLEA

Sanatan ya fadi haka ne ta cikin sanarwar da hadiminsa, Olaitan Adeyanju ya fitar a ranar Litinin a matsayin martani kan zargin da NDLEA ta yi masa.

NDLEA
Sanata Oyelola Ashiru ya musanta ta'ammali da miyagun kwayoyo Hoto: Nigerian Senate/NDLEA
Asali: Facebook

Jaridar The Cable ta wallafa cewa hukumar NDLEA ta bayyana gano wasu miyagun kwayoyi a gidan Sanatan bayan jami'anta sun kai sumame.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"NDLEA ta yi karya:" Sanata Ashiru

Jaridar The Nation ta tattaro cewa Sanatan da NDLEA ke zargi an kama kwayoyi a gidansa ya musanta cewa shi ya dauki hadiman da aka ce an gano.

A sanarwar da hadimin Sanata Oyelola Yisa Ashiru ya fitar, ya bayyana cewa babu masu sunan Ibrahim Mohammd da Mohammed Yahaya a cikin hadiman Sanatan.

Sanata ya nemi NDLEA ta tafi kotu

Sanatan Kwara ya shawarci hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi da ta gaggauta kai wadanda ta ce an kama a gidansa a gaban kotu idan da gaske ne.

Kara karanta wannan

Rigimar APC ta sake dagulewa da Sanata Wamakko da Lamido suka ja ɓangarensu

Sanata Oyelolo Ashiru ya ce tabbas jami'an NDLEA sun binciki gidansa da ke Kwara, kuma ba a samu wani abin laifi ba kamar yadda hukumar ke ikirari.

"Mun kama kwaya a gidan Sanata:" NDLEA

A baya mun wallafa cewa shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi, Birgediya Janar Buba Marwa mai ritaa ya ce an kama miyagun kwayoyi a gidan Sanata Oyelola Ashiru.

Wannan na zuwa bayan Sanata Ashiru a nemi majalisar dattawa ta amince a ruguje hukumar biyo bayan samun lam'a kan yadda ta ke gudanar da ayyukanta na yaki da safarar kwaya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.