Musulmai Sun Magantu kan Zargin Shirin Rushe Masallacin Juma'a, Sun ba Gwamna Shawara

Musulmai Sun Magantu kan Zargin Shirin Rushe Masallacin Juma'a, Sun ba Gwamna Shawara

  • Kungiyar Kuteb Muslim Development Association (KMDA) ta yi magana kan zargin shirin rushe masallacin Juma'a
  • Kungiyar ta yi Allah wadai da shirin rushe masallacin Juma'a a karamar hukumar Takum da ke jihar
  • Shugaban kungiyar, Alhaji Bako Mairiga ya bukaci Gwamna Agbu Kefas ya dauki matakin gaggawa kan lamarin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Taraba - Kungiyar Musulmai ta yi martani kan zargin shirin rusa babban masallacin Juma'a a jihar Taraba.

Kungiyar Kuteb Muslim Development Association (KMDA) a karamar hukumar Takum ta yi Allah wadai da lamarin.

Musulmai sun yi Allah wadai da zargin shirin rushe masallacin Juma'a
Kungiyar Musulmai ta shawarci Gwamna Agbu Kefas kan zargin shirin rushe masallacin Juma'a a Taraba. Hoto: Agbu Kefas.
Asali: Twitter

Ƙungiya ta magantu kan zargin rushe masallaci

Shugaban kungiyar, Alhaji Bako Mairiga shi ya bayyana haka a yau Lahadi 20 ga watan Oktoban 2024 a Jalingo, cewar Tribune.

Kara karanta wannan

Yadda ‘yan siyasar jihar Kano 4 suka zagaya kujera 1 cikin shekaru 8 a gwamnatin tarayya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mairiga ya ce zargin shirin rushe babban masallacin Juma'a a Takum karan-tsaye ne ga Musulman Kuteb.

Ya ce gari irin Takum da ya sha fama da rikice-rikice a baya bai kamata a sake jefa shi matsala da tashin hankali ba.

Kungiyar Musulmai ta shawarci Gwamna Agbu Kefas

Kungiyar ta bukaci Gwamna Agbu Kefas da ya tabbatar ba a cigaba da shirin rushe masallacin ba domin samun zaman lafiya.

"Ukwe Ahmadu a matsayinsa na Musulmi ya ga dacewar gina masallacin Juma'a kusa da fada a shekarar 1912 saboda shi da sauran Musulmai su yi ibada a wurin."
"A matsayinmu na kungiya masu son zaman lafiya muna ganin rushe masallacin da fadar Takum zai kawo rudani da tashin hankali."

- Alhaji Bako Mairiga

Kungiyar ta kuma musanta zargin cewa Kuteb sun rusa masallaci da kuma hallaka wasu daga cikin masallata.

Kara karanta wannan

An nada dan kabilar Ibo na farko a matsayin babban limanin masallacin Abuja

Gwamna ya musanta shirin rushe masallacin Juma'a

Kun ji cewa Gwamnatin jihar Taraba ta musanta zargin cewa ta na shirin rusa fadar Takum da babban Masallacin Juma'a a garin.

Kwamishinar yaɗa labarai, Zainab Usman Jalingo ta ce zargin ba shi da tushe, inda ta bukaci mutane su yi watsi da shi.

Tun farko dai kungiyar Kuteb ta Najeriya watau KYN ta zargi gwamnatin Agbu Kefas da yunkurin rusa wuraren na tarihi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.