Tochukwu: Abubuwa 5 game da Ɗan Kabilar Ibo da Ya Zama Limamin Masallacin Abuja

Tochukwu: Abubuwa 5 game da Ɗan Kabilar Ibo da Ya Zama Limamin Masallacin Abuja

Abuja - Farfesa Iliyasu Usman, dan kabilar Igbo na farko da aka nada a matsayin limamin babban masallacin Abuja, ya gabatar da hudubarsa ta farko a ranar Juma’a.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

An rahoto cewa nadin Farfesa Iliyasu a matsayin daya daga cikin limamai na babban masallacin kasa ya jawo kalaman yabo daga jama'a musamman kungiyar SEMON.

Abubuwan da ya kamata ku sani game da sabon limamin masallacin Abuja.
Farfesan Larabci da wasu abubuwa 5 da ya kamata ku sani game da sabon limamin masallacin Abuja. Hoto: @PeterObi
Asali: Twitter

Jaridar Tribune Online ta bayyana abubuwa biyar da ya kamata a sani game da sabon limamin babban masallacin Juma'ar na Abuja.

1. Farfesan Larabci na farko daga Ibo

Farfesa Illyas ne farfesan Larabci na farko daga kasar Ibo, wanda ya bayyana irin nasarorin da ya samu a fannin ilimi da kuma gudunmawar da ya bayar ga ilimin addinin Musulunci.

Kara karanta wannan

Babban limamin Imo ya bayyana kalubalen da Musulmi ke fuskanta a Kudu maso Gabas

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

2. Ya shiga tawagar limamai

Farfesa Illyas ya shiga sahun limaman masallacin Abuja da ke jagoranci a yanzu; Farfesa Ibrahim Makari da Farfesa Muhammad Kabir.

Kasancewar a yanzu limamin masallacin na hudu Sheikh Ahmad Onilewura yana jinya, limaman uku ne za su rika jagorantar sallar Juma'a da Khamsus Salawati biyar.

3. Ya samu goyon bayan SEMON

Kungiyar Musulmin Kudu Maso Gabashin Najeriya (SEMON) ta goyi bayan nadin Farfesa Illyas matsayin limamin babban masallacin Abuja.

Jaridar Aminiya, ta rahoto SEMON a wata sanarwa da ta fitar ta ce:

"Wannan gagarumin matsayi ba sheda ce ta sadaukar da kai da kwazonka na ilimi kadai ba, wani nauyi ne da ya rataya a wuyanka na jagorantar al'umma zuwa ga bautar Allah."

4. Tauraron hadin kan al'ummar Musulmi

Da dama na kallon Farfesa Illyas a matsayin tauraro wanda nadinsa ya zama wata shaida da ke nuna hadin kan al'ummar Musulmi tare da kore wariya ta kabilanci.

Kara karanta wannan

Rikicin APC ya ƙara ƙamari, babban basarake a Arewa ya yi murabus daga sarauta

Mutane sun yabawa majalisar koli ta harkokin addinin musulunci ta Najeriya NSCIA karkashin sarkin musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar kan wannan nadi.

5. Hudubarsa ta farko

Bayan nadin nasa, Farfesa Ilyas Usman ya gabatar da hudubarsa ta farko a matsayin daya daga cikin Limamin Masallacin kasa a ranar 18 ga Oktoba 2024.

An nada dan ibo limamin Abuja

A wani labarin, mun ruwaito cewa mahukunta sun amince da nadin Farfesa Iliyasu Usman a matsayin sabon limanin babban masallacin Juma'a na Abuja.

Farfesa Iliyasu Usman ya shiga tarihin wannan masallaci, inda ya zamo dan kabilar Ibo na farko da ya rike mukamin babban limamin masallacin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.