Bayan Shafe Makonni 2, Shugaban Kasa Bola Tinubu Ya Dawo Najeriya

Bayan Shafe Makonni 2, Shugaban Kasa Bola Tinubu Ya Dawo Najeriya

  • Jirgin da ya kai shugaban Najeriya Birtaniya domin yin hutun makonni biyu ya dawo da shi da yamman nan
  • A ranar Asabar fadar shugaban kasa ta tabbatar da cewa Bola Ahmed Tinubu ya iso birnin tarayya watau Abuja
  • Hadimin shugaba Bola Tinubu ya nuna bidiyon dawowarsa a shafinsa, lokacin hutun da ya dauka ya kare

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Abuja - Mai girma shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya dawo Najeriya bayan shafe kwanaki ya na hutu a ketare.

Rahotanni sun tabbatar da cewa jirgin shugaban Najeriyan ya iso ne a yammacin Asabar, sai ba a kai ga ganinsa ba.

Tinubu
Shugaban Kasa Bola Tinubu ya iso Najeriya Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Shugaba Bola Tinubu ya sauka a Abuja

Mai taimakawa Bola Ahmed Tinubu a kafofin sadarwa na zamani, Olusegun Dada ya tabbatar da hakan a shafinsa na X.

Kara karanta wannan

Tinubu ya fadi wanda ke ba shi shawara tun bayan hawansa mulki, ya yaba masa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Olusegun Dada ya yi magana ya na mai nuna jirgin fadar shugaban Najeriya ya sauka.

‘Barka da zuwa shugaban kasa’

- Olusegun Dada

Yaushe Tinubu ya iso Najeriya?

An tabbatar da wannan zance da kimanin karfe 7:20 na yammacin yau 19 ga watan Oktoba dandalin sada zumuntan.

Wasu bidiyo biyu da aka wallafa sun nuna jirgin shugaban kasar ya na sauka a filin tashi da saukar jiragen sama a Abuja.

A wani gajeren bidiyon kuma an ga mutane su na fareti cikin duhu domin tarbar shugaban kasa kamar dai yadda aka saba.

Hutun Tinubu a Turai ya kare

Rahoton The Cable ya ce shugaba Bola Tinubu ya dawo gida ne bayan ya dauki makonni biyu ya na hutawa a Birtaniya.

Idan za a tuna, Tinubu ya bar Najeriya ne a farkon watan Oktoban nan, ya yi kwanaki 17 tsakanin kasashen Ingila da Faransa.

Ministocin Tinubu sun sha kenan?

Kara karanta wannan

‘Yan APC da suka koma kuka da gwamnati saboda tsadar rayuwa a zamanin Tinubu

Ana sa rai zuwa ranar Litinin a ga shugaban kasan a ofis, kuma watakila zai iya jagorantar zaman majalisar zartarwa (FEC).

An dai ta yada cewa Tinubu zai iya amfani da damar wannan tafiya da ya yi domin yin canji a majalisar ministocin tarayya.

Masoyan APC da ke sukar Tinubu

An kawo rahoton 'yan APC da suka koma sukar gwamnatin Bola Tinubu. Alal Joe Igbokwe ya na cikin masoyan APC a baya.

Sukar gwamnatin Bola Tinubu ne ya jawo Muhammad Ali Ndume ya rasa matsayinsa a majalisa kuma har yau bai daina.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng