Bayan Shafe Makonni 2, Shugaban Kasa Bola Tinubu Ya Dawo Najeriya

Bayan Shafe Makonni 2, Shugaban Kasa Bola Tinubu Ya Dawo Najeriya

  • Jirgin da ya kai shugaban Najeriya Birtaniya domin yin hutun makonni biyu ya dawo da shi da yamman nan
  • A ranar Asabar fadar shugaban kasa ta tabbatar da cewa Bola Ahmed Tinubu ya iso birnin tarayya watau Abuja
  • Hadimin shugaba Bola Tinubu ya nuna bidiyon dawowarsa a shafinsa, lokacin hutun da ya dauka ya kare

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Abuja - Mai girma shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya dawo Najeriya bayan shafe kwanaki ya na hutu a ketare.

Rahotanni sun tabbatar da cewa jirgin shugaban Najeriyan ya iso ne a yammacin Asabar, sai ba a kai ga ganinsa ba.

Tinubu
Shugaban Kasa Bola Tinubu ya iso Najeriya Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

Shugaba Bola Tinubu ya sauka a Abuja

Mai taimakawa Bola Ahmed Tinubu a kafofin sadarwa na zamani, Olusegun Dada ya tabbatar da hakan a shafinsa na X.

Kara karanta wannan

Tinubu ya fadi wanda ke ba shi shawara tun bayan hawansa mulki, ya yaba masa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Olusegun Dada ya yi magana ya na mai nuna jirgin fadar shugaban Najeriya ya sauka.

‘Barka da zuwa shugaban kasa’

- Olusegun Dada

Yaushe Tinubu ya iso Najeriya?

An tabbatar da wannan zance da kimanin karfe 7:20 na yammacin yau 19 ga watan Oktoba dandalin sada zumuntan.

Wasu bidiyo biyu da aka wallafa sun nuna jirgin shugaban kasar ya na sauka a filin tashi da saukar jiragen sama a Abuja.

A wani gajeren bidiyon kuma an ga mutane su na fareti cikin duhu domin tarbar shugaban kasa kamar dai yadda aka saba.

Hutun Tinubu a Turai ya kare

Rahoton The Cable ya ce shugaba Bola Tinubu ya dawo gida ne bayan ya dauki makonni biyu ya na hutawa a Birtaniya.

Idan za a tuna, Tinubu ya bar Najeriya ne a farkon watan Oktoban nan, ya yi kwanaki 17 tsakanin kasashen Ingila da Faransa.

Kara karanta wannan

‘Yan APC da suka koma kuka da gwamnati saboda tsadar rayuwa a zamanin Tinubu

Ministocin Tinubu sun sha kenan?

Ana sa rai zuwa ranar Litinin a ga shugaban kasan a ofis, kuma watakila zai iya jagorantar zaman majalisar zartarwa (FEC).

An dai ta yada cewa Tinubu zai iya amfani da damar wannan tafiya da ya yi domin yin canji a majalisar ministocin tarayya.

Masoyan APC da ke sukar Tinubu

An kawo rahoton 'yan APC da suka koma sukar gwamnatin Bola Tinubu. Alal Joe Igbokwe ya na cikin masoyan APC a baya.

Sukar gwamnatin Bola Tinubu ne ya jawo Muhammad Ali Ndume ya rasa matsayinsa a majalisa kuma har yau bai daina.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng