Gwamnan APC Ya Ciri Tuta, Ya Sanar da Sabon Albashin da Zai Fara Biyan Ma'aikata

Gwamnan APC Ya Ciri Tuta, Ya Sanar da Sabon Albashin da Zai Fara Biyan Ma'aikata

  • Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ya yi alƙawarin biyan ma'aikata N85,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi nan ba da daɗewa ba
  • Gwamna Sanwo-Olu ya ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi ranar Laraba, 16 ga watan Oktoba, 2024
  • Babajide Sanwo-Olu na jam'iyyar APC ya zama gwamna na farko da ya yi alƙawarin kai albashi mafi karanci N100,000 a 2025

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Lagos - Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta biya N85,000 a matsayin sabon mafi karancin albashi ga ma'aikata.

Gwamnan ya sanar da haka ne ranar Laraba, 16 ga watan Oktoba, 2024, inda ya ce nan da wasu ƴan watanni zai ƙara albashin zuwa N100,000.

Kara karanta wannan

Gwamna ya kafa tarihi, ya shirya biyan mafi ƙarancin albashin N100,000, ya fadi dalilai

Gwamna Sanwo Olu.
Gwamnan jihar Legas ya shirya kara mafi karancin albashi zuwa N100,000 Hoto: Babajide Sanwo-Olu
Asali: Facebook

Babajide Sanwo Olu ya bayyana haka ne a wata hira da gidan talabijin na Channels tv ranar Laraba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnan Legas ya haura albashin N70,000

Idan baku manta ba gwamnatin tarayya da ƴan kwadago sun amince da N70,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa.

Amma bayan haka wasu jihohin sun yi ƙari a kan haka domin inganta walwala da jin daɗin ma'aikatan gwamnati.

Da yake jawabi, Gwamna Sanwo-Olu ya ce gwamnatinsa a shirye take ta kara mafi karancin albashi zuwa N100,000 a watan Janairun 2025.

Gwamnan ya ce ma'aikata sun cancanci a rika biyansu albashin da zai ɗauke ɗawainiyar su da ta iyalansu a wata.

Sanwo-Olu zai fara biyan ma'aikata N85,000

Sanwo-Olu ya ce:

"Dangane da mafi karancin albashi da na ji kun ambata, ina mai farin cikin sanar da cewa mu da ƴan kwadago mun cimma matsayar biyan N85,000."

Kara karanta wannan

Gwamnan PDP ya umarci biyan mafi ƙarancin albashin N70,000 nan take

"Wannan ba wani abu ba ne, ba zan tsaya ina cewa muna biyan albashi fiye da wasu jihohi ba, magana ce ta gwargwadon abin da kowa zai iya."

Majalisa ta dakatar da ciyaman a Legas

A wani labarin kuma majalisar dokokin jihar Legas ta dakatar da shugaban ƙaramar hukumar Alimosho, Jelili Sulaimon, daga kan muƙaminsa.

A cewar ƴan majalisar, dakatarwar da aka yi wa shugaban ƙaramar hukumar za ta fara aiki ne nan take ba tare da ɓata wani lokaci ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262