Yan Fashi Sun Mamaye Unguwa Tsakar Dare, Sun bi Gida Gida Suna Ta’addanci

Yan Fashi Sun Mamaye Unguwa Tsakar Dare, Sun bi Gida Gida Suna Ta’addanci

  • Wasu yan fashi da makami sun mamaye wata unguwa cikin dare inda suka rika bi gida gida suna yi wa al'umma ta'addanci
  • Mutanen unguwar sun ce yan fashin yi gayya, kuma sun yi harbe harbe, ba su tsaya nan ba, sun sace dukiya mai dimbin yawa
  • Bayan wayewar gari, an tafi da mutanen da yan fashin suka yi wa harbi da sara da adduna zuwa asibiti domin jinya da karɓar magani

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Akwa Ibom - Al'umma sun kwana cikin tashin hankali a unguwar Ifa Atai Etoi na birnin Uyo a jihar Akwa Ibom.

Yan fashi da makami ne suka yi mamaya a unguwar cikin dare su na bi gida bayan gida su na sata da harbe harbe.

Kara karanta wannan

An kona gidan mai unguwa da ofishin yan sanda kan garkuwa da mutane

Akwa Ibom
Yan fashi sun kai hari Akwa Ibom. Hoto: Legit
Asali: Original

Jaridar the Nation ta wallafa cewa yan fashi da makamin sun bar mutanen unguwar da mummunar asara.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yan fashi sun mamaye unguwa a Uyo

A daren Litinin ne miyagu yan fashi da makami suka rika bi gida gida suna sata da harbin mutane a wata unguwa a jihar Akwa Ibom.

Wasu mazauna unguwar sun bayyanawa cewa miyagun shigo gidansu da misalin karfe 1:30 na dare wasu kuma da misalin karfe 2:00 na dare.

Yan fashi sun yi ta'adi a unguwa

Wani da abin ya shafa ya ce mutane sun kai 15 suka shiga gidansa kuma sun fara da harbin matarsa a kafa, suka ce idan ya yi motsi za su harbe shi.

Yan fashin sun yi sara da adda a kayin wani mai gadi mai suna Victor wanda yanzu haka yana asibiti domin karɓar magani.

Kara karanta wannan

'Akwai matsala': Yadda malami 1 ke koyar da daruruwan dalibai a makarantun gwamnati

Kayan da yan fashi suka sace a Uyo

Rahotanni sun nuna cewa yan fashi da makamin sun sace wayoyin hannu da dama, na'ura mai ƙwaƙwalwa, miliyoyin kudi da sauransu.

A yanzu haka dai an sanar da rundunar yan sanda saboda gudanar da bincike ko za a gano miyagun da suka yi ta'asar.

An kona caji ofis a jihar Edo

A wani rahoton, kun ji cewa an samu barkewar mummunar rikici kan zargin garkuwa da mutane da wasu matasa suka yi a jihar Edo.

Rahotanni sun nuna cewa wasu matasa ne da suke zargin ana garkuwa da yan uwansu suka tunkari ofishin yan sanda, suka kona shi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng