An Shiga Tashin Hankali da Wani Gini Mai Hawa 2 Ya Rufta, Bidiyo Ya Bayyana

An Shiga Tashin Hankali da Wani Gini Mai Hawa 2 Ya Rufta, Bidiyo Ya Bayyana

  • Mutane sun yi takansu yayin da wani bene mai hawa biyu ya rufta da safiyar ranar Litinin, 14 ga watan Oktoba, 2024 a Legas
  • Rahotanni sun nuna cewa dukkan mutanen da ke zaune a benen sun yi takansu gabanin faruwar mummunan lamarin a yau
  • A rahoton farko da ta tattara, hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Legas ta ce babu wanda ya rasa ransa a rugujewar ginin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Lagos - Wani gini mai hawa biyu ya ruguje a kan layin Amusu da ke unguwar Orile Iganmu a jihar Legas da sanyin safiyar yau Litinin, 14 ga watan Oktoba, 2024.

Wani faifan bidiyo mai ta da hankali da ake yaɗawa a soshiyal midiya ya nuna yadda ginin ya rufta ba zato ba tsammani.

Kara karanta wannan

An rasa rayuka yayin da tireloli suka murkushe masu keke Napep

Taswirar Legas.
Gini.mai hawa 2 ya rufta a jihar Lehas, LESEMA ta ce babu wanda ya mutu Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Jaridar Leadership ta tattaro cewa mutanen da ke wurin sun yi rige-rigen guduwa domin neman tsira a lokacin da suka fahimci ginin na shirin ruftawa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda ginin ya ruguje a Legas

Bidiyon da aka naɗa ya nuna lokacin da mutane suka fara tsere domin neman mafaka bayan ginin ya fara ƙarar rugujewa.

A rahoton masaniyar farko da hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Legas watau LASEMA ta fitar, ta ce babu wanda ya mutu sakamakon rushewar ginin.

Jami'in hulɗa da jama'a na LASEMA, Nosa Okunbor ya ce dukkan mutanen da ke cikin ginin sun fita salin-alin gabannin ya kai ga ruahewa.

Jami'an LASEMA sun kai ɗauki

Ya ce tuni tawagar ba da agaji da ceto suka isa wurin domin fara lalube ko wani ya maƙale a ɓaraguzan ginin, rahoton Daily Trust.

Kara karanta wannan

'Akwai matsala': Yadda malami 1 ke koyar da daruruwan dalibai a makarantun gwamnati

Okunbor ya ce:

"Jami'anmu da tawagar ƴan kwana-kwana da rundunar ƴan sanda sun kai ɗauki wurin domin jawo hankalin mutane su tashi daga kewayen ginin da ya rufta don kaucewa wata matsalar."

Gobara ta babbake gidajen ma'aikata a Legas

Rahotanni sun bayyana cewa gobara ta babbake rukunin gidajen ma'aikatan gwamnatin jihar Legas da ke Odunsanmi a Ogba.

An tattaro cewa gobarar ta babbake wani gida mai hawa har uku da wani gida mai dakuna biyu da sauran wasu gidajen a Legas.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262