DSS Ta Shiga Tsakani kan Rigimar Kungiyar IPMAN da NNPCL, an Samu Matsaya

DSS Ta Shiga Tsakani kan Rigimar Kungiyar IPMAN da NNPCL, an Samu Matsaya

  • A karshe, hukumar tsaro ta farin kaya, DSS ta shiga tsakani kan rigimar kungiyar IPMAN da kamfanin NNPCL
  • Daraktan hukumar DSS, Adeola Ajayi shi ya bukaci ganawar domin dinke barakar da ke tsakaninsu game da farashin man fetur
  • Daga ƙarshe, an samu mafita a tsakaninsu yayin ganawar da ta samun halartar shugaban NNPCL, Mele Kyari dana IPMAN, Abubakar Maigandi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Yayin da ake rigima tsakanin kamfanin NNPCL da dillalan mai, hukumar DSS ta shiga lamarin.

Shugaban hukumar, Adeola Ajayi shi ya bukaci zama na musamman da bangarorin biyu domin samun mafita.

Hukumar DSS ta yi ganawa da NNPCL da IPMAN kan rigimar da ke tsakaninsu
Hukumar DSS sasanta rikicin kungiyar IPMAN da kamfanin NNPCL. Hoto: NNPC Limited.
Asali: Facebook

An yi ganawa tsakanin IPMAN da NNPCL

Kara karanta wannan

Shugaban kamfanin NNPCL, Kyari ya yi babban rashi, Kashim Shettima ya jajanta

Sakataren yada labaran ƙungiyar IPMAN, Chinedu Ukadike shi ya tabbatar da haka ga jaridar Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ukadike ya ce ganawar ta samu halartar shugaban hukumar NMDPRA da kuma na kamfanin NNPCL, Mele Kyari.

Ya ce musabbabin ganawar akwai matsalar farashi tsakaninsu da matatar Dangote da kuma rashin siyarwa IPMAN kaya.

"Daraktan hukumar DSS ya gayyace mu ganawa ta musamman domin samun matsaya kan rigimar IPMAN da NNPCL."
"Musabbabin ganawar shi ne rashin bin ka'idar siyar da kaya ga IPMAN da kuma matsalar farashi tsakaninmu da NNPCL."
"An samu matsaya a ganawar karkashin jagorancin shugaban IPMAN, Abubakar Maigandi cewa NNPCL ta amince da ba kungiyar damar daukar kaya."

- Chinedu Ukadike

Karanta karin wasu labaran kan NNPCL, IPMAN:

Kara karanta wannan

Damagum: Kotu ta dakile kwamitin gudanarwar PDP, ta ba da sabon umarni

NNPCL ya janye shiga tsakanin Dangote da IPMAN

Kun ji cewa Kamfanin mai na NNPCL ya tsame kansa daga shiga tsakani a harkar kasuwancin man fetur a matatar Aliko Dangote.

Kamfanin ya dauki matakin domin gudun biyan raran kudi yayin da ya ke shiga tsakanin dillalan mai da matatar Dangote.

Wasu masana sun yi hasashen ba dillalan mai damar alaka kai tsaye da matatar Dangote ka iya kara farashin fetur a ƙasa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.