Gwamna Ya Faranta Ran Ma'aikata, Zai Biya N73,000 a Matsayin Mafi Karancin Albashi

Gwamna Ya Faranta Ran Ma'aikata, Zai Biya N73,000 a Matsayin Mafi Karancin Albashi

  • Gwamnan jihar Ondo, Lucky Orimisan Aiyedatiwa ya amince zai biya ma'aikata sabon mafi ƙarancin albashi
  • Gwamna Aiyedatiwa ya bayyana cewa zai biya ma'aikatan jihar N73,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashi
  • Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen gwamna na APC a zaɓen jihar da ke tafe a watan Nuwamban 2024

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Ondo - Gwamnan Ondo kuma ɗan takarar jam’iyyar APC a zaɓen gwamnan jihar da za a gudanar ranar 16 ga watan Nuwamba, Lucky Aiyedatiwa, ya amince da biyan sabon mafi ƙarancin albashi.

Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya amince zai biya ma'aikatan jihar mafi ƙarancin albashi na N73,000. 

Gwamnan Ondo ya amince da mafi karancin albashi
Gwamna Aiyedatiwa ya amince zai biya N73,000 a matsayin mafi karancin albashi Hoto: Lucky Orimisan Aiyedatiwa
Asali: Facebook

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa Gwamna Aiyedatiwa ya bayyana hakan ne a wajen ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen gwamna na APC a ƙaramar hukumar Ondo ta Yamma a ranar Asabar.

Kara karanta wannan

Soke hukumar EFCC: Gwamna ya saba da takwarorinsa, ya ba da shawara

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Aiyedatiwa zai biya ma'aikata N73,000

Gwamnan ya samu rakiyar mataimakinsa, Cif Olayide Adelami da manyan jiga-jigan jam'iyyar APC, rahoton jaridar Tribune ya tabbatar.

Gwamna Aiyedatiwa ya bayyana cewa gwamnatinsa tana ba da muhimmanci kan jin daɗin ma'aikatan jihar.

"Muna zaburar da ma’aikatanmu ta hanyar kawo shirye-shiryen horarwa daban-daban, kuma ana biyansu albashi a kan lokaci."
"Ba a biyo mu bashi kuma bari na sanar da ku cewa wannan gwamnatin ta yanke shawarar aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi."
"Duk da cewa mafi ƙarancin albashi ya kamata ya zama N70,000, namu zai kasance N73,000. Za mu ci gaba da inganta jin daɗin ku. Zuwa ranar 16 ga watan Nuwamba, 2024, ku fito ku zaɓi APC."

- Gwamna Lucky Aiyedatiwa

Gwamnan Oyo zai biya albashin N70,000

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya bayar da tabbacin cewa gwamnatinsa za ta fara biyan mafi ƙarancin albashi na N70,000.

Gwamna Seyi Makinde ya bayyana cewa zai fara biyan mafi ƙarancin albashin da zarar an daidaita batun ƙarin da za a yi a albashin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng