Gwamna Zulum Ya Amince da Sabon Mafi Karancin Albashi, Ya Sa Lokacin Fara Biya

Gwamna Zulum Ya Amince da Sabon Mafi Karancin Albashi, Ya Sa Lokacin Fara Biya

  • Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya amince da fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi ga ma'aikata
  • A cikin sanarwar da hadimin Zulum ya fitar, ya ce za a fara biyan ma'aikata mafi ƙarancin albashin ne a watan Oktoban 2024
  • Abdulrahman Ahmed Bundi ya ƙara da cewa gwamnan zai biya basussukan kuɗaɗen giratuti da ake bin gwamnatin Borno

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Borno - Gwamnan Borno, Babagana Zulum, ya yi magana kan biyan ma'aikatan gwamnatin jihar sabon mafi ƙarancin albashi.

Gwamna Babagana Zulum ya bayyana cewa jihar za ta fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi daga wannan watan na Oktoba.

Zulum ya amince da sabon mafi karancin albashi
Gwamna Zulum zai fara biyan mafi karancin albashi a Oktoba Hoto: @govborno
Asali: Facebook

Babban mataimaki na musamman ga gwamnan kan kafafen yaɗa labaran zamani, Abdulrahman Ahmed Bundi, ya bayyana hakan a shafinsa na Facebook a ranar Alhamis.

Kara karanta wannan

Gwamnan APC ya kori hadiminsa na musamman, an gano dalilin sallamar

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Zulum zai biya mafi ƙarancin albashi

Abdulrahman Bundi ya ce Gwamna Zulum ya yi taro da kwamitin aiwatar da mafi ƙarancin albashi na jihar, inda ya ba da umarnin a biya ma’aikatan gwamnati sabon albashin.

"An gudanar da taron ne a Maiduguri ranar Litinin a zauren majalisar da ke gidan gwamnati."

- Abdulrahman Ahmed Bundi

Zulum zai biya hakkokin ma'aikatan Borno

Hakazalika Abdulrahman Bundi ya ce Gwamna Zulum ya amince da fitar da N3bn domin biyan iyalan ma'aikatan da suka rasu a jihar Borno haƙƙoƙinsu.

Zulum ya kuma ba da tabbacin cewa zai biya basussukan kuɗaɗen giratuti da aka biyo jihar bashi tare da tabbatar da sake duba abin da ƴan fansho ke karba.

Karanta wasu labaran kan mafi ƙarancin albashi

Kara karanta wannan

Gwamnan Zamfara ya yi alhinin kisan jami'an tsaro, ya ba da tabbaci

Gwamna Zulum ya fara rabon tallafi

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan Borno, Babagana Umaru Zulum, ya kaddamar da rabon kayan tallafi a hukumance ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri.

Yayin ƙaddamar da shirin a Maiduguri, Farfesa Zulum ya ce za a fara rabon kayan tallafin da magidanta 5,235 a Gwange 1 da ke ƙaramar hukumar birni.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng