'Ka Biya Mu daga Tushe', Sarakuna a Arewa Sun Roki Tinubu kan Biyansu Hakkokinsu

'Ka Biya Mu daga Tushe', Sarakuna a Arewa Sun Roki Tinubu kan Biyansu Hakkokinsu

  • Wasu sarakunan gargajiya a Najeriya sun nuna damuwa kan yadda ake samun matsala game da kudin da ake ware musu
  • Sarakuna daga jihar Nassarawa sun bukaci Gwamnatin Tarayya ta rika ba su kasonsu na 5% daga tushe domin yin adalci
  • Wannan na zuwa ne bayan korafi kan yadda ake hada musu kason nasu a kudin ƙananan hukumomi wanda ake samun matsala

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Sarakunan gargajiya a Najeriya sun roki Gwamnatin Tarayya alfarma kan kason kudi da ake ba su.

Sarakunan sun bukaci biyansu kudi 5% da aka ware musu na musamman a rika biyansu daga tushe.

Kara karanta wannan

Farashin fetur: Ministar Tinubu ta yi albishir mai daɗi ga yan Najeriya

Sarakunan gargajiya sun roki Tinubu alfarma kan kudin da ake ba su
Sarakunan gargajiya a Arewa sun nuna damuwa kan yadda kasonsu daga Gwamnatin Tarayya ke makalewa. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

Sarakuna sun roki Tinubu kan hakkokinsu

Leadership ta ce daman ana haɗawa sarakunan ne a cikin kudin kananan hukumomi domin ba su kasonsu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Chun Mada na Akwanga, Dakta Samson Gamu shi ya roki Gwamnatin Tarayya a madadin sauran sarakunan gargajiya a jihar Nasarawa.

Basaraken ya bayyana haka yayin da suka kai wa shugaban Hukumar tattarawa da raba kudi a Najeriya, RMAFC, Mohamed Bello Shehu a Abuja.

Sarakunan sun yabawa shugaba Bola Tinubu kan yadda ya himmatu wurin tabbatar da yancin kananan hukumomi, The Nation ta ruwaito.

"Duk da samun cigaba da aka yi kan 5% na sarakunan gargajiya, ana fuskantar matsala wurin isowar kudin inda ya dace."
"Ba mu amince da yadda ake cire kudin ba domin babu adalci da bayyana komai a fili."

- Sarakunan gargajiya

Gwamnatin Tarayya ta yabawa sarakunan gargajiya

Kara karanta wannan

Tinubu ya fadi dalilin kawo manufofin tattalin da suka jawo wahalar rayuwa

Shugaban hukumar RMAFC, Mohamed Bello Shehu ya bayyana muhimmancin sarakunan gargajiya a cikin al'umma.

Bello Shehu ya ce sarakunan ba iya bangaren al'adu suke taka rawa ba har ma da kasancewa jagororin kawo cigaba a kasa.

Gwamnoni na kokarin dakile yancin kananan hukumomi

Kun ji cewa Majalisar dattawa ta yi wata ganawa ta musamman a Abuja kan abin da ya shafi samun yancin kananan hukumomi a Najeriya.

Majalisar ta zargi wasu gwamnoni da hada baki da Majalisun jihohinsu domin kwace kudin kananan hukumomi daga Gwamnatin Tarayya.

Wannan na zuwa ne yayin da wasu gwamnoni ke kokarin kakaba wata doka a jihohinsu domin karkatar da kudin kananan hukumomi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.