"Wasu ba Su Jin Dadi": Shehu Sani kan Kokarin Matawalle a Yaki da Ta'addanci

"Wasu ba Su Jin Dadi": Shehu Sani kan Kokarin Matawalle a Yaki da Ta'addanci

  • Tsohon sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani ya yabawa karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle kan yaki da ta'addanci
  • Shehu Sani ya kuma bukaci al'umma da su bar sukar Matawalle da Nuhu Ribadu inda ya ce hakan na kawo cikas a yaki da ta'addanci
  • Sanatan ya bukaci al'umma da su cigaba da ba da goyon baya domin ganin an kawo karshen rikicin ba sukar juna ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kaduna - Tsohon sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani ya magantu kan matsalar ta'addanci a Arewa.

Shehu Sani ya ce abin takaici ne yadda ake sukar ƙaramin Ministan tsaro, Bello Matawalle da Nuhu Ribadu kan lamarin.

Kara karanta wannan

Wike ya ba 'ya 'yan Buhari, manyan ƴan siyasa wa'adin mako 2 kan filayensu a Abuja

Shehu Sani ya yabawa Matawalle da Nuhu Ribadu kan yaki da ta'addanci
Shehu Sani shawarci al'umma su ba da goyon baya wurin dakile matsalolin tsaro. Hoto: Shehu Sani.
Asali: Facebook

Shehu Sani ya caccaki masu sukar Matawalle

Tsohon sanatan ya bayyana haka yayin ganawa da yan jaridu a jihar Kaduna, kamar yadda Punch ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanatan ya ce sukar Matawalle da Ribadu yana kawo tsaiko a kokarin dakile hare-haren yan bindiga.

Shehu Sani ya ce tabbas a yanzu ana kokari musamman a yaki da ta'addanci inda ya tabbatar da cewa an fara yin galaba a kansu.

Ta'addanci: Shehu Sani ya kan masu kawo cikas

Ya nuna damuwa kan yadda wasu tsiraru ba su jin dadin yadda ake hallaka kasurguman yan bindiga a yankin.

"Yanzu da ake samun nasara kan yan bindiga, ya kamata Janar Christopher Musa da Bello Matawalle da Nuhu Ribadu su mayar da hankali sosai kada su bari a kawar musu da hankali."
"Duk wanda ke burin a kawo karshen wadannan miyagu dole ya ba da goyon baya wurin dakile matsalar madadin suka da bai da amfani."

Kara karanta wannan

An fatattaki mutumi a masallacin Abuja bayan ya zo Musulunta, an gano makircinsa

- Shehu Sani

2027: Shehu Sani ya roki yan Arewa

Kun ji cewa Shehu Sani ya bayyana cewa kamata ya yi Arewa ta hakura ta bar ƴan Kudu su ci gaba da mulkin Najeriya a babban zaɓen 2027.

Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya ya ce daga nan kuma Arewa za ta samu cikakkiyar damar samar da shugaban ƙasa a 2031.

Ya ƙara da cewa Bola Tinubu ya cancanci ya kara samun goyon bayan ƴan Arewa saboda abin da ya yi masu lokacin zaben 2015.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.