Wike: Cikakken Jerin Manyan 'Yan Siyasa 60 da Za Su Iya Rasa Filayensu a Birnin Abuja

Wike: Cikakken Jerin Manyan 'Yan Siyasa 60 da Za Su Iya Rasa Filayensu a Birnin Abuja

Abuja - Hukumar FCTA za ta sa kafar wando daya da wasu daidaikun mutane da kamfanoni a babban birnin tarayya Abuja.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

FCTA ta na barazanar karbe takardun shaidar mallakar wasu filaye da ke unguwar Maitama idan ba su biya bashin kudinsu ba.

Abuja
FCTA za ta iya karbe filayen mutane a Abuja Hoto: Zahra Buhari
Asali: Facebook

FCTA za ta iya raba mutane da filayensu

Rahoton Punch ya bayyana cewa an yi wa masu filayen barazana a ranar Juma’a cewa za su iya rasa kasarsu idan har suka yi sake.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Abin da ya sa ake so a biya kudin shi ne domin gwamnati ta cigaba da ayyukan more rayuwa a shiyyar Maitama II (A10) a birnin Abuja.

Kara karanta wannan

Ganduje ya bayyana wanda ya ceci jam’iyyar APC daga asarar Naira biliyan 1.5

Legit Hausa ta bibiyi jerin da Premium Times ta kawo, ta tattaro sunayen wadanda abin ya shafa a karkashin jagorancin Nyesom Wike.

‘Ya ‘yan manyan da ke cikin matsala a Abuja

1. Yusuf Buhari

2. Zahra Buhari

Manyan gwamnati da za su iya rasa filaye

3. Shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajudeen

4. Sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume

5. Shugaban fadar ma’aikatan gidan gwamnati, Femi Gbajabiamila

Tsofaffin shugabannin majalisa

6. Ameh Ebute

7. Bukola Saraki

8. Yakubu Dogara

9. Ovie Omo-Agege

Ministocin gwamnati na cikin matsala a Abuja

10. Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo

11. Ministan wasanni, John Eno

12. Ministan noma, Abubakar Kyari

Tsofaffin sanatoci, gwamnoni da ministoci

13. Chris Nigige

14. Theodore Orji

15. Rochas Okorocha

16. Ibikunle Amosun

17. Tanko Al-Makura

18. Joshua Dariye

19. Gabriel Suswam

20. Ibrahim Shekarau

21. Okezie Ikpeazu

22. Jonah Jang

23. Adamu Muazu

24. Marigayi Bukar Abba Ibrahim

25. Dino Melaye

26. Kabiru Marafa

27. Stella Oduah

28. Ben Bruce

29. David Umaru

30. Biodun Olujimi

31. Andy Uba

32. Emmanuel Bwacha

33. Kabiru Gaya

34. Peter Nwaoboshi

35. Philip Aduda

Kara karanta wannan

Cikakken jerin abubuwa 63 da Gwamnatin Tinubu ta cirewa harajin VAT

36. Binta Garba

37. Teslim Folarin

38. Darlington Nwokocha

39. Smart Adeyemi

40. Ben Obi

41. Abdullahi Adamu

FCTA za ta iya karbe filayen Sanatoci masu-ci

42. Danjuma Goje

43. Saliu Mustapha

44. Sunday Karimi

45. Ali Ndume

46. Osita Izunaso

47. Seriake Dickson

48. Chukwuka Utazi

49. Oker Jev

Tsofaffi da ‘yan majalisar wakilai masu-ci

50. Olumide Osoba

51. Nicholas Ossai

52. Wole Oke

53. Julius Ihonvbere

54. Khadijat Ibrahim

55. Lynda Ikpeazu

56. Obinna Chidoka

57. Beni Lar

58. Leo Ogor

59. Timothy Golu

60. Edward Pwajok

'Yan siyasar da za su iya yakar Tinubu

A wani rahoto, an ji cewa akwai wasu ’yan siyasar Kudancin Najeriya da ka iya neman takawa Bola Tinubu burki a zaben 2027.

Wasu ’yan siyasar kudancin kasar nan na iya kalubalantar shugaba Bola Tinubu. Daga cikinsu akwai Peter Obi da Nyesom Wike.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng